< Karin Magana 16 >

1 Ga mutum ne shirye-shiryen zuciya suke, amma daga Ubangiji ne amshin harshe kan zo.
The preparations of the heart in man, and the answer of the tongue, [is] from the LORD.
2 Dukan hanyoyin mutum sukan yi kamar marar laifi ne gare shi, amma Ubangiji yakan auna manufofi.
All the ways of a man [are] clean in his own eyes; but the LORD weigheth the spirits.
3 Ka miƙa wa Ubangiji dukan abin da kake yi, shirye-shiryenka kuwa za su yi nasara.
Commit thy works unto the LORD, and thy thoughts shall be established.
4 Ubangiji yana yin kome domin amfaninsa, har ma da mugaye domin ranar masifa.
The LORD hath made all [things] for himself: yea, even the wicked for the day of evil.
5 Ubangiji yana ƙyamar dukan zuciya mai girman kai. Ka tabbata da wannan. Ba za su kuɓuta daga hukunci ba.
Every one [that is] proud in heart [is] an abomination to the LORD: [though] hand [join] in hand, he shall not be unpunished.
6 Ta wurin ƙauna da aminci akan yi kafarar zunubi; ta wurin tsoron Ubangiji mutum kan guji mugunta.
By mercy and truth iniquity is purged: and by the fear of the LORD [men] depart from evil.
7 Sa’ad da hanyoyin mutum sun gamshi Ubangiji, yakan sa abokan gāban mutumin ma su zauna lafiya da shi.
When a man’s ways please the LORD, he maketh even his enemies to be at peace with him.
8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar adalci da sami riba mai yawa ta hanyar rashin gaskiya.
Better [is] a little with righteousness than great revenues without right.
9 ’Yan Adam sukan yi shirye-shiryensu a zukatansu, amma Ubangiji ne yake da ikon cika matakansa.
A man’s heart deviseth his way: but the LORD directeth his steps.
10 Leɓunan sarki kan yi magana kamar ta wurin ikon Allah, kuma bai kamata bakinsa ya yi kuskure a yanke shari’a ba.
A divine sentence [is] in the lips of the king: his mouth transgresseth not in judgment.
11 Ma’aunai da magwajin gaskiya daga Ubangiji ne; dukan ma’aunai da suke cikin jaka yinsa ne.
A just weight and balance [are] the LORD’s: all the weights of the bag [are] his work.
12 Sarakuna suna ƙyamar abin da ba shi da kyau, gama an kafa kujerar sarauta ta wurin adalci ne.
[It is] an abomination to kings to commit wickedness: for the throne is established by righteousness.
13 Sarakuna sukan ji daɗi leɓuna masu yin gaskiya; sukan darjanta mutumin da yake faɗin gaskiya.
Righteous lips [are] the delight of kings; and they love him that speaketh right.
14 Fushin sarki ɗan saƙon mutuwa ne, amma mai hikima yakan faranta masa rai.
The wrath of a king [is as] messengers of death: but a wise man will pacify it.
15 Sa’ad da fuskar sarki ta haska, yana nufin rai ke nan; tagomashinsa yana kamar girgijen ruwa a bazara.
In the light of the king’s countenance [is] life; and his favour [is] as a cloud of the latter rain.
16 Ya ma fi kyau ka sami hikima fiye da zinariya, ka zaɓi fahimi a maimakon azurfa!
How much better [is it] to get wisdom than gold! and to get understanding rather to be chosen than silver!
17 Buɗaɗɗiyar hanyar masu aikata gaskiya kan guje wa mugunta; duk wanda yake lura da hanyarsa yakan lura da ransa.
The highway of the upright [is] to depart from evil: he that keepeth his way preserveth his soul.
18 Girmankai yakan zo kafin hallaka, girman kai yakan zo kafin fāɗuwa.
Pride [goeth] before destruction, and an haughty spirit before a fall.
19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu sauƙinkai, da ka raba ganima da masu girman kai.
Better [it is to be] of an humble spirit with the lowly, than to divide the spoil with the proud.
20 Duk wanda ya mai da hankali ga umarni yakan yi nasara, kuma mai albarka ne wanda yake dogara ga Ubangiji.
He that handleth a matter wisely shall find good: and whoso trusteth in the LORD, happy [is] he.
21 Akan ce da masu hikima a zuciya hazikai, kuma kalmomi masu daɗi kan inganta umarni.
The wise in heart shall be called prudent: and the sweetness of the lips increaseth learning.
22 Fahimi shi ne maɓulɓular rai ga waɗanda suke da shi, amma wauta kan kawo hukunci ga wawaye.
Understanding [is] a wellspring of life unto him that hath it: but the instruction of fools [is] folly.
23 Zuciyar mai hikima kan bi da bakinsa, kuma leɓunansa kan inganta umarni.
The heart of the wise teacheth his mouth, and addeth learning to his lips.
24 Kalmomi masu daɗi suna kama da kakin zuma, mai zaƙi ga rai da kuma warkarwa ga ƙasusuwa.
Pleasant words [are as] an honeycomb, sweet to the soul, and health to the bones.
25 Akwai hanyar da ta yi kamar daidai ga mutum, amma a ƙarshe takan kai ga mutuwa.
There is a way that seemeth right unto a man, but the end thereof [are] the ways of death.
26 Marmarin cin abinci yakan yi wa ɗan ƙodago aiki; yunwarsa kan sa ya ci gaba.
He that laboureth laboureth for himself; for his mouth craveth it of him.
27 Mutumin banza yakan ƙulla mugunta, kuma jawabinsa yana kama da wuta mai ƙuna.
An ungodly man diggeth up evil: and in his lips [there is] as a burning fire.
28 Fitinannen mutum yakan zuga tashin hankali, mai gulma kuma yakan raba abokai na kusa.
A froward man soweth strife: and a whisperer separateth chief friends.
29 Mutum mai tā-da-na-zaune-tsaye yakan ruɗi maƙwabcinsa ya kai shi a hanyar da ba ta da kyau.
A violent man enticeth his neighbour, and leadeth him into the way [that is] not good.
30 Duk wanda ya ƙyifce da idonsa yana ƙulla maƙarƙashiya ce; duk wanda ya murguɗa leɓunansa yana niyya aikata mugunta ke nan.
He shutteth his eyes to devise froward things: moving his lips he bringeth evil to pass.
31 Furfura rawani ne mai daraja; akan same ta ta wurin yin rayuwa ta adalci.
The hoary head [is] a crown of glory, [if] it be found in the way of righteousness.
32 Gara ka zama mai haƙuri da ka zama jarumi, ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane.
[He that is] slow to anger [is] better than the mighty; and he that ruleth his spirit than he that taketh a city.
33 Akan jefa ƙuri’a a kan cinya, amma kowace shawara mai kyau daga Ubangiji ne.
The lot is cast into the lap; but the whole disposing thereof [is] of the LORD.

< Karin Magana 16 >