< Filibbiyawa 2 >

1 In kuna da wata ƙarfafawa daga tarayya da Kiristi, in da wata ta’aziyya daga ƙaunarsa, in da wani zumunci da Ruhu, in da juyayi da tausayi,
If, then, any encouragement comes through union with Christ, if there is any persuasive power in love, if there is any communion with the Spirit, if there is any tenderness or pity,
2 to, sai ku sa farin cikina yă zama cikakke ta wurin kasance da hali ɗaya, kuna ƙauna ɗaya, kuna zama ɗaya cikin ruhu da kuma manufa.
I entreat you to make my happiness complete – live together animated by the same spirit and in mutual love, one in heart, animated by one Spirit.
3 Kada ku yi kome da sonkai ko girman kai, sai dai cikin tawali’u, ku ɗauki waɗansu sun fi ku.
Nothing should be done out of selfish ambition or vain conceit. Rather, in humility lift others up above yourselves,
4 Bai kamata kowannenku yă kula da sha’anin kansa kawai ba, sai dai yă kula da sha’anin waɗansu ma.
considering not only your own interests but also the interests of others.
5 A cikin dangantakarku da juna, ya kamata halayenku su zama kamar na Kiristi Yesu.
Let the spirit of Christ Jesus be yours also.
6 Wanda, ko da yake cikin ainihin surar Allah yake, bai mai da daidaitakansa nan da Allah wani abin riƙewa kam-kam ba,
Though the divine nature was his from the beginning, yet he did not look on equality with God as above all things to be clung to,
7 amma ya mai da kansa ba kome ba, yana ɗaukan ainihin surar bawa, aka yi shi cikin siffar mutum.
but impoverished himself by taking the nature of a servant and becoming like one of us;
8 Aka kuma same shi a kamannin mutum, ya ƙasƙantar da kansa ya kuma zama mai biyayya wadda ta kai shi har mutuwa, mutuwar ma ta gicciye!
he appeared among us as a man, and still further humbled himself by submitting even to death – to death on a cross!
9 Saboda haka Allah ya ɗaukaka shi zuwa mafificin wuri ya kuma ba shi sunan da ya fi dukan sunaye,
And that is why God raised him to the very highest place, and gave him the name which stands above all other names,
10 don a sunan Yesu kowace gwiwa za tă durƙusa, a sama da a ƙasa da kuma a ƙarƙashin ƙasa,
so that in adoration of the name of Jesus every knee should bend, in heaven, on earth, and under the earth,
11 kowane harshe kuma yă furta cewa Yesu Kiristi Ubangiji ne, don ɗaukakar Allah Uba.
and that every tongue should acknowledge JESUS CHRIST as LORD – to the glory of God the Father.
12 Saboda haka, ya abokaina ƙaunatattu, kamar yadda kullum kuke biyayya ba kawai sa’ad da ina nan ba, amma yanzu da ba na nan tare da ku, ku ci gaba da yin ayyukan cetonku da tsoro da kuma rawan jiki,
Therefore, my dear friends, as you have always been obedient in the past, so now work out your own salvation with anxious care, not only when I am with you, but all the more now that I am absent.
13 gama Allah ne yake aiki a cikinku, don ku nufa ku kuma aikata bisa ga nufinsa mai kyau.
Remember it is God who, in his kindness, is at work within you, enabling you both to will and to work.
14 Ku yi kome ba tare da gunaguni ko gardama ba,
In all that you do, avoid murmuring and dissension,
15 don ku zama marasa abin zargi, sahihai’ya’yan Allah, waɗanda ba su da laifi, a zamanin mutane karkatattu, kangararru, waɗanda kuke haskakawa a cikinsu kamar fitilu a duniya
so as to prove yourselves blameless and innocent – faultless children of God, in the midst of an evil-disposed and perverse generation, in which you are seen shining like stars in a dark world,
16 kuna kuwa cin gaba da riƙe maganar rai domin in yi taƙama a ranar Kiristi cewa ban yi gudu ko fama a banza ba.
offering to them the message of life; and then I will be able at the day of Christ to boast that I did not run my course for nothing, or toil for nothing.
17 Amma ko da ana tsiyaye jinina kamar hadaya ta sha a kan hadaya da kuma hidimar da take fitowa daga bangaskiyarku, ina murna ina kuma farin ciki da ku duka.
And yet, even if, when your faith is offered as a sacrifice to God, my lifeblood must be poured out in addition, still I will rejoice and share the joy of you all;
18 Haka ma ya kamata ku yi murna ku kuma yi farin ciki tare da ni.
and you must also rejoice and share my joy.
19 Ina sa rai a cikin Ubangiji Yesu cewa zan aika da Timoti zuwa gare ku ba da daɗewa ba, don ni ma in ji daɗi sa’ad da na ji labarinku.
I hope, however, as one who trusts in the Lord Jesus, to send Timothy to you before long, so that I may myself be cheered by receiving news of you.
20 Ba ni da wani kamar sa, wanda yake da ainihin sha’awa a zaman lafiyarku.
For I have no one but him to send – no one of kindred spirit who would take the same genuine interest in your welfare.
21 Gama kowa yana lura da al’amuran kansa ne kawai, ba na Kiristi Yesu ba.
They are all pursuing their own aims and not those of Christ Jesus.
22 Amma, ai, kun san darajar Timoti yadda muka yi bautar bishara tare, kamar ɗa da mahaifinsa.
But you know what Timothy has proved himself to be, and how, like a child working for his father, he worked hard with me in spreading the good news.
23 Saboda haka, ina sa rai, in aike shi da zarar na ga yadda abubuwa suke a nan.
It is Timothy, then, whom I hope to send, just as soon as I find out what is going to happen to me here.
24 Ni kuma ina da tabbaci a cikin Ubangiji cewa zan zo ba da daɗewa ba.
And I am confident, as one who trusts in the Lord Jesus, that before long I myself will follow.
25 Amma ina gani ya dace in aika da Afaforiditus, ɗan’uwana, abokin aikina da kuma abokin famana, wanda kuma yake ɗan saƙonku, wanda kuka aika domin yă biya mini bukatuna.
Still I think it necessary to send Epaphroditus to you now, for he is my dear friend, fellow worker, and fellow soldier, and he was also your messenger to help me in my need.
26 Gama yana marmarin ganinku duka ya kuma damu domin kun ji cewa ya yi rashin lafiya.
For he has been longing to see you all, and has been distressed because you heard of his illness.
27 Ba shakka ya yi rashin lafiya, har ya kusa mutuwa. Amma Allah ya nuna masa jinƙai, ba shi kaɗai ba amma har da ni ma, don yă rage mini baƙin ciki kan baƙin ciki.
And I can assure you that his illness very nearly proved fatal. But God had pity on him, and not on him only but also on me, so that I might not have sorrow on sorrow.
28 Saboda haka na yi niyya ƙwarai in aike shi wurinku, don sa’ad da kuka sāke ganinsa za ku yi murna, ni kuma in rage damuwa.
I am all the more ready, therefore, to send him, so that the sight of him may revive your spirits and my own sorrow be lightened.
29 Ku marabce shi cikin Ubangiji da farin ciki mai yawa, ku kuma girmama mutane irinsa,
Give him, then, the heartiest of Christian welcomes, and hold such people in great honour.
30 domin ya kusa yă mutu saboda aikin Kiristi, ya yi kasai da ransa don yă cikasa taimakon da ba ku iya yi mini ba.
For it was owing to his devotion to the Master’s work that he was at the point of death, having risked his own life in the effort to supply what was wanting in the help that you sent me.

< Filibbiyawa 2 >