< Ƙidaya 26 >

1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
Or il arriva, après cette plaie, que l'Éternel dit à Moïse et à Éléazar, fils d'Aaron, le sacrificateur:
2 “Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
Faites le compte de toute l'assemblée des enfants d'Israël, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, selon les maisons de leurs pères, tous ceux d'Israël qui peuvent aller à la guerre.
3 Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
Moïse et Éléazar, le sacrificateur, leur parlèrent donc dans les plaines de Moab, près du Jourdain de Jérico, en disant:
4 “Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
Qu'on fasse le dénombrement depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, comme l'Éternel l'a commandé à Moïse et aux enfants d'Israël, sortis du pays d'Égypte.
5 Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
Ruben, premier-né d'Israël. Fils de Ruben: Hénoc; de lui sort la famille des Hénokites; de Pallu, la famille des Palluites;
6 daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
De Hetsron, la famille des Hetsronites; de Carmi, la famille des Carmites.
7 Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
Telles sont les familles des Rubénites; et ceux dont on fit le dénombrement furent quarante-trois mille sept cent trente.
8 Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
Et les fils de Pallu: Éliab.
9 ’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
Et les fils d'Éliab: Némuël, Dathan et Abiram. C'est ce Dathan et cet Abiram, convoqués à l'assemblée, qui se soulevèrent contre Moïse et contre Aaron, dans l'assemblée de Coré, quand ils se soulevèrent contre l'Éternel,
10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
Et que la terre ouvrit sa bouche et les engloutit, avec Coré, alors que ceux qui s'étaient assemblés moururent, quand le feu dévora les deux cent cinquante hommes et qu'ils servirent d'exemple.
11 Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
Mais les fils de Coré ne moururent point.
12 Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
Fils de Siméon, selon leurs familles: de Némuël, la famille des Némuélites; de Jamin, la famille des Jaminites; de Jakin, la famille des Jakinites;
13 daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
De Zérach, la famille des Zérachites; de Saül, la famille des Saülites.
14 Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
Telles sont les familles des Siméonites: vingt-deux mille deux cents.
15 Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
Fils de Gad, selon leurs familles: de Tséphon, la famille des Tséphonites; de Haggi, la famille des Haggites; de Shuni, la famille des Shunites;
16 daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
D'Ozni, la famille des Oznites; d'Éri, la famille des Érites;
17 daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
D'Arod, la famille des Arodites; d'Aréli, la famille des Arélites.
18 Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
Telles sont les familles des fils de Gad, selon leur dénombrement: quarante mille cinq cents.
19 Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
Fils de Juda: Er et Onan; mais Er et Onan moururent au pays de Canaan.
20 Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
Les fils de Juda, selon leurs familles, furent: de Shéla, la famille des Shélanites; de Pharets, la famille des Phartsites; de Zérach, la famille des Zérachites.
21 Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
Et les fils de Pharets furent: de Hetsron, la famille des Hetsronites; et de Hamul, la famille des Hamulites.
22 Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
Telles sont les familles de Juda, selon leur dénombrement: soixante et seize mille cinq cents.
23 Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
Fils d'Issacar, selon leurs familles: de Thola, la famille des Tholaïtes; de Puva, la famille des Puvites;
24 daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
De Jashub, la famille des Jashubites; de Shimron, la famille des Shimronites.
25 Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
Telles sont les familles d'Issacar, selon leur dénombrement: soixante-quatre mille trois cents.
26 Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
Fils de Zabulon, selon leurs familles: de Séred, la famille des Sardites; d'Élon, la famille des Élonites; de Jahléel, la famille des Jahléélites.
27 Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
Telles sont les familles des Zabulonites, selon leur dénombrement: soixante mille cinq cents.
28 Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
Fils de Joseph, selon leurs familles: Manassé et Éphraïm.
29 Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
Fils de Manassé: de Makir, la famille des Makirites; et Makir engendra Galaad; de Galaad, la famille des Galaadites.
30 Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
Voici les fils de Galaad: de Jézer, la famille des Jézerites; de Hélek, la famille des Helkites;
31 daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
D'Asriel, la famille des Asriélites; de Sichem, la famille des Sichémites;
32 daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
De Shémida, la famille des Shémidaïtes; de Hépher, la famille des Héphrites.
33 (Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
Or, Tselophcad, fils de Hépher, n'eut point de fils, mais des filles. Et les noms des filles de Tselophcad étaient: Machla, Noa, Hogla, Milca et Thirtsa.
34 Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
Telles sont les familles de Manassé, et leur dénombrement fut de cinquante-deux mille sept cents.
35 Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
Voici les fils d'Éphraïm, selon leurs familles: de Shuthélach, la famille des Shuthélachites; de Béker, la famille des Bakrites; de Thachan, la famille des Thachanites.
36 Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
Et voici les fils de Shuthélach: d'Éran, la famille des Éranites.
37 Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
Telles sont les familles des fils d'Éphraïm, selon leur dénombrement: trente-deux mille cinq cents. Ce sont là les fils de Joseph, selon leurs familles.
38 Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
Fils de Benjamin, selon leurs familles: de Béla, la famille des Balites; d'Ashbel, la famille des Ashbélites; d'Achiram, la famille des Achiramites;
39 daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
De Shéphupham, la famille des Shuphamites; de Hupham, la famille des Huphamites.
40 Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
Les fils de Béla furent Ard et Naaman; d'Ard, la famille des Ardites; de Naaman, la famille des Naamites.
41 Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
Tels sont les fils de Benjamin, selon leurs familles; et leur dénombrement fut de quarante-cinq mille six cents.
42 Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
Voici les fils de Dan, selon leurs familles: de Shucham, la famille des Shuchamites. Ce sont là les familles de Dan, selon leurs familles;
43 Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
Toutes les familles des Shuchamites, selon leur dénombrement, furent soixante-quatre mille quatre cents.
44 Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
Fils d'Asser, selon leurs familles: de Jimma, la famille des Jimmites; de Jishvi, la famille des Jishvites; de Beria, la famille des Beriites.
45 daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
Des fils de Beria: de Héber, la famille des Hébrites; de Malkiel, la famille des Malkiélites.
46 (Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
Et le nom de la fille d'Asser, était Sérach.
47 Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
Telles sont les familles des fils d'Asser, selon leur dénombrement: cinquante-trois mille quatre cents.
48 Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
Fils de Nephthali, selon leurs familles: de Jahtseel, la famille des Jahtséelites; de Guni, la famille des Gunites;
49 daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
De Jetser, la famille des Jitsrites; de Shillem, la famille des Shillémites.
50 Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
Telles sont les familles de Nephthali, selon leurs familles; et leur dénombrement fut de quarante-cinq mille quatre cents.
51 Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
Tels sont ceux des enfants d'Israël dont on fit le dénombrement: six cent un mille sept cent trente.
52 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l'Éternel parla à Moïse, en disant:
53 “Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
Le pays sera partagé entre ceux-ci en héritage, selon le nombre des noms;
54 Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
A ceux qui sont en grand nombre, tu donneras plus d'héritage, et à ceux qui sont en petit nombre, tu donneras moins d'héritage; on donnera à chacun son héritage en proportion de son recensement.
55 Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
Mais le pays sera partagé par le sort; ils recevront leur héritage selon les noms des tribus de leurs pères.
56 Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
L'héritage de chacun sera déterminé par le sort, en ayant égard au grand nombre ou au petit nombre.
57 Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
Voici les Lévites dont on fit le dénombrement, selon leurs familles: de Guershon, la famille des Guershonites; de Kéhath, la famille des Kéhathites; de Mérari, la famille des Mérarites.
58 Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
Voici les familles de Lévi: la famille des Libnites, la famille des Hébronites, la famille des Machlites, la famille des Mushites, la famille des Corhites. Or Kéhath engendra Amram.
59 sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
Et le nom de la femme d'Amram était Jokébed, fille de Lévi, qui naquit à Lévi en Égypte; elle enfanta à Amram, Aaron, Moïse et Marie leur sœur.
60 Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
Et à Aaron, naquirent Nadab et Abihu, Éléazar et Ithamar.
61 Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
Mais Nadab et Abihu moururent en offrant un feu étranger devant l'Éternel.
62 Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
Or ceux des Lévites qu'on dénombra furent vingt-trois mille, tous mâles, depuis l'âge d'un mois et au-dessus; car ils ne furent point dénombrés avec les enfants d'Israël, parce qu'il ne leur fut point donné d'héritage au milieu des enfants d'Israël.
63 Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
Tel est le dénombrement fait par Moïse et Éléazar; le sacrificateur, qui dénombrèrent les enfants d'Israël dans les campagnes de Moab, près du Jourdain de Jérico;
64 Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
Et parmi ceux-ci il n'y avait aucun de ceux qui avaient été dénombrés par Moïse et Aaron, le sacrificateur, quand ils firent le dénombrement des enfants d'Israël au désert de Sinaï;
65 Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
Car l'Éternel avait dit d'eux: Ils mourront dans le désert; et il n'en resta pas un, excepté Caleb, fils de Jephunné, et Josué, fils de Nun.

< Ƙidaya 26 >