< Ƙidaya 26 >

1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya yi magana da Musa da Eleyazar ɗan Haruna, firist ya ce,
Et il arriva, après la plaie, que l’Éternel parla à Moïse et à Éléazar, fils d’Aaron, le sacrificateur, disant:
2 “Ku ƙidaya dukan jama’ar Isra’ila daga mai shekaru ashirin zuwa gaba da za su iya aikin sojan Isra’ila.”
Relevez la somme de toute l’assemblée des fils d’Israël, depuis l’âge de 20 ans et au-dessus, selon leurs maisons de pères, tous ceux qui sont propres au service militaire en Israël.
3 Musa da Eleyazar firist suka yi musu magana a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko, suka ce,
Et Moïse, et Éléazar, le sacrificateur, leur parlèrent dans les plaines de Moab, près du Jourdain de Jéricho, disant: …
4 “Ku ƙidaya maza daga mai shekara ashirin zuwa gaba yadda Ubangiji ya umarci Musa.” Waɗannan su ne Isra’ilawan da suka fito daga Masar.
Depuis l’âge de 20 ans et au-dessus, comme l’Éternel le commanda à Moïse et aux fils d’Israël, qui sortirent du pays d’Égypte.
5 Zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila, daga Hanok; kabilar Hanokawa; daga Fallu; kabilar Falluyawa;
Ruben, le premier-né d’Israël. Les fils de Ruben: [de] Hénoc, la famille des Hénokites; de Pallu, la famille des Palluites;
6 daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Karmi, kabilar Karmiyawa.
de Hetsron, la famille des Hetsronites; de Carmi, la famille des Carmites.
7 Waɗannan su ne kabilan Ruben; jimillarsu ta kai 43,730.
– Ce sont là les familles des Rubénites; et leurs dénombrés furent 43 730.
8 Ɗan Fallu kuwa shi ne Eliyab,
– Et les fils de Pallu: Éliab;
9 ’ya’yan Eliyab maza kuwa su ne, Nemuwel, Datan da Abiram. Datan da Abiram nan, su ne shugabannin mutanen da suka tayar wa Musa da Haruna, suna kuma cikin waɗanda suka bi Kora sa’ad da ya tayar wa Ubangiji.
et les fils d’Éliab: Nemuel, et Dathan, et Abiram. C’est ce Dathan et cet Abiram, des principaux de l’assemblée, qui se soulevèrent contre Moïse et contre Aaron dans l’assemblée de Coré, lorsqu’ils se soulevèrent contre l’Éternel;
10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora, wanda ƙungiyarsa ta mutu sa’ad da wuta ta cinye mutum 250. Wannan kuwa ya zama alamar faɗakarwa.
et la terre ouvrit sa bouche et les engloutit, ainsi que Coré, lorsque l’assemblée mourut, quand le feu dévora les 250 hommes; et ils furent pour signe.
11 Amma fa, zuriyar Kora ba tă mutu ba.
Mais les fils de Coré ne moururent pas.
12 Zuriyar Simeyon bisa ga kabilansu, daga Nemuwel, kabilar Nemuwelawa; daga Yamin, kabilar Yaminawa; daga Yakin, kabilar Yakinawa;
Les fils de Siméon, selon leurs familles: de Nemuel, la famille des Nemuélites; de Jamin, la famille des Jaminites; de Jakin, la famille des Jakinites;
13 daga Zera, kabilar Zerawa; daga Sha’ul, kabilar Sha’ul.
de Zérakh, la famille des Zarkhites; de Saül, la famille des Saülites.
14 Waɗannan su ne kabilan Simeyon; jimillarsu ta kai 22,200.
– Ce sont là les familles des Siméonites, 22 200.
15 Zuriyar Gad bisa ga kabilansu, daga Zafon, kabilar Zafonawa; daga Haggi, kabilar Haggiwa; daga Shuni, kabilar Shunawa;
Les fils de Gad, selon leurs familles: de Tsephon, la famille des Tsephonites; de Haggui, la famille des Hagguites; de Shuni, la famille des Shunites;
16 daga Ozni, kabilar Ozniyawa daga Eri, kabilar Eriyawa;
d’Ozni, la famille des Oznites; d’Éri, la famille des Érites;
17 daga Arod, kabilar Arodiyawa; daga Areli, kabilar Areliyawa.
d’Arod, la famille des Arodites; d’Areéli, la famille des Areélites.
18 Waɗannan su ne kabilan Gad, jimillarsu ta kai 40,500.
– Ce sont là les familles des fils de Gad, selon leur dénombrement, 40 500.
19 Er da Onan,’ya’yan Yahuda ne, amma sun mutu a Kan’ana.
Les fils de Juda: Er et Onan; et Er et Onan moururent dans le pays de Canaan.
20 Zuriyar Yahuda bisa ga kabilansu, daga Shela, kabilar Shelayawa daga Ferez, kabilar Ferezawa; daga Zera, kabilar Zerawa;
Et les fils de Juda, selon leurs familles: de Shéla, la famille des Shélanites; de Pérets, la famille des Partsites; de Zérakh, la famille des Zarkhites.
21 Zuriyar Ferez kuwa, daga Hezron, kabilar Hezronawa; daga Hamul; kabilar Hamulawa.
Et les fils de Pérets: de Hetsron, la famille des Hetsronites; de Hamul, la famille des Hamulites.
22 Waɗannan su ne kabilan Yahuda; jimillarsu ta kai 76,500.
– Ce sont là les familles de Juda, selon leur dénombrement, 76 500.
23 Zuriyar Issakar bisa ga kabilansu, daga Tola, kabilar Tolatawa; daga Fuwa, kabilar Fuwayawa;
Les fils d’Issacar, selon leurs familles: [de] Thola, la famille des Tholaïtes; de Puva, la famille des Punites;
24 daga Yashub, kabilar Yashubawa; daga Shimron, kabilar Shimronawa.
de Jashub, la famille des Jashubites; de Shimron, la famille des Shimronites.
25 Waɗannan su ne kabilan Issakar; jimillarsu ta kai 64,300.
– Ce sont là les familles d’Issacar, selon leur dénombrement, 64 300.
26 Zuriyar Zebulun bisa ga kabilansu, daga Sered, kabilar Seredawa; daga Elon kabilar Elonawa; daga Yaleyel; kabilar Yaleyewa.
Les fils de Zabulon, selon leurs familles: de Séred, la famille des Sardites; d’Élon, la famille des Élonites; de Jakhleël, la famille des Jakhleélites.
27 Waɗannan su ne kabilan Zebulun, jimillarsu ta kai 60,500.
– Ce sont là les familles des Zabulonites, selon leur dénombrement, 60 500.
28 Zuriyar Yusuf bisa ga kabilansu ta wurin Manasse da Efraim.
Les fils de Joseph, selon leurs familles, Manassé et Éphraïm.
29 Zuriyar Manasse, daga Makir, kabilar Makiriyawa (Makir shi ne mahaifin Gileyad); daga Gileyad, kabilar Gileyadawa.
– Les fils de Manassé: de Makir, la famille des Makirites; et Makir engendra Galaad; de Galaad, la famille des Galaadites.
30 Waɗannan su ne zuriya Gileyad, daga Iyezer, kabilar Iyezerawa; daga Helek, kabilar Helekawa;
– Ce sont ici les fils de Galaad: [d’]Ihézer, la famille des Ihézrites; de Hélek, la famille des Helkites;
31 daga Asriyel, kabilar Asriyelawa; daga Shekem, kabilar Shekem;
d’Asriel, la famille des Asriélites; [de] Sichem, la famille des Sichémites;
32 daga Shemida, kabilar Shemadawa; daga Hefer, kabilar Heferawa.
[de] Shemida, la famille des Shemidaïtes; [de] Hépher, la famille des Héphrites.
33 (Zelofehad ɗan Hefer, ba shi da’ya’ya maza;’yan mata ne kaɗai ya haifa, sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.)
– Et Tselophkhad, fils de Hépher, n’eut pas de fils, mais des filles; et les noms des filles de Tselophkhad étaient: Makhla, et Noa, Hogla, Milca, et Thirtsa.
34 Waɗannan su ne kabilan Manasse, jimillarsu ta kai 52,700.
– Ce sont là les familles de Manassé; et leurs dénombrés, 52 700.
35 Waɗannan su ne kabilan Efraim bisa ga kabilansu, daga Shutela, kabilar Shutelawa; daga Beker, kabilar Bekerawa; daga Tahan, kabilar Tahanawa.
Ce sont ici les fils d’Éphraïm, selon leurs familles: de Shuthélakh, la famille des Shuthalkhites; de Béker, la famille des Bacrites; de Thakhan, la famille des Thakhanites.
36 Waɗannan su ne kabilan Shutelawa, daga Eran, kabilar Eranawa.
– Et ce sont ici les fils de Shuthélakh: d’Éran, la famille des Éranites.
37 Waɗannan su ne kabilan Efraim; jimillarsu ta kai 32,500. Waɗannan su ne kabilan Yusuf ta wurin kabilansu.
– Ce sont là les familles des fils d’Éphraïm, selon leur dénombrement, 32 500. – Ce sont là les fils de Joseph, selon leurs familles.
38 Zuriyar Benyamin bisa ga kabilansu, daga Bela, kabilar Belawa; daga Ashbel, kabilar Ashbelawa; daga Ahiram, kabilar Ahiramawa;
Les fils de Benjamin, selon leurs familles: de Béla, la famille des Balites; d’Ashbel, la famille des Ashbélites; d’Akhiram, la famille des Akhiramites;
39 daga Shufam, kabilar Shufamawa; daga Hufam, kabilar Hufamawa.
de Shephupham, la famille des Shuphamites; de Hupham, la famille des Huphamites.
40 Zuriyar Bela daga Ard da Na’aman, daga Ard, kabilar Ardawa; daga Na’aman, kabilar Na’amawa;
– Et les fils de Béla furent Ard et Naaman: [d’Ard], la famille des Ardites; de Naaman, la famille des Naamites.
41 Waɗannan su ne kabilan Benyamin, jimillarsu ta kai 45,600.
– Ce sont là les fils de Benjamin, selon leurs familles; et leurs dénombrés, 45 600.
42 Waɗannan su ne kabilan Dan bisa ga kabilarsu, daga Shuham, kabilar Shuhamawa. Waɗannan su ne kabilan Dan.
Ce sont ici les fils de Dan, selon leurs familles: de Shukham, la famille des Shukhamites. Ce sont là les familles de Dan, selon leurs familles.
43 Dukansu kabilan Shuhamawa ne, jimillarsu ta kai 64,400.
– Toutes les familles des Shukhamites, selon leur dénombrement, 64 400.
44 Zuriyar Asher bisa ga kabilansu, daga Imna, kabilar Imnawa daga Ishbi, kabilar Ishbiyawa; daga Beriya, kabilar Beriyawa;
Les fils d’Aser, selon leurs familles: de Jimna, la famille des Jimna; de Jishvi, la famille des Jishvites; de Beriha, la famille des Berihites.
45 daga zuriyar Beriya kuwa, daga Heber, kabilar Heberawa; daga Malkiyel, kabilar Malkiyelawa.
– Des fils de Beriha: de Héber, la famille des Hébrites; de Malkiel, la famille des Malkiélites.
46 (Asher yana da’ya mace da ake kira Sera.)
– Et le nom de la fille d’Aser était Sérakh.
47 Waɗannan su ne kabilan Asher; jimillarsu ta kai 53,400.
Ce sont là les familles des fils d’Aser, selon leur dénombrement, 53 400.
48 Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;
Les fils de Nephthali, selon leurs familles: de Jahtseël, la famille des Jahtseélites; de Guni, la famille des Gunites;
49 daga Yezer, kabilar Yezerawa; daga Shillem, kabilar Shillemawa.
de Jétser, la famille des Jitsrites; de Shillem, la famille des Shillémites.
50 Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.
– Ce sont là les familles de Nephthali, selon leurs familles; et leurs dénombrés, 45 400.
51 Dukan jimillar mazan Isra’ila ta kai 601,730.
Ce sont là les dénombrés des fils d’Israël, 601 730.
52 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l’Éternel parla à Moïse, disant:
53 “Ka rarraba musu ƙasar a matsayin gādo, bisa ga yawan kabila.
Le pays sera partagé à ceux-ci en héritage, selon le nombre des noms.
54 Ga ƙungiya mafi girma, ka ba ta rabo mafi girma; ga ƙaramar ƙungiya kuwa, ka ba ta ƙarami rabo; kowane zai karɓa rabonsa ga yawan mutanen da aka rubuta.
À ceux qui sont nombreux, tu augmenteras l’héritage; et à ceux qui sont peu nombreux, tu diminueras l’héritage: tu donneras à chacun son héritage en proportion de ses dénombrés.
55 Ka tabbatar an rarraba ƙasar ta wurin rabo. Abin da kowace ƙungiya ta gāda zai zama bisa ga sunayen kabilar kakanninta.
Seulement, le pays sera partagé par le sort; ils l’hériteront selon les noms des tribus de leurs pères.
56 Za a raba kowane gādo bisa ga rabo tsakanin manyan da ƙanana ƙungiyoyi.”
C’est selon la décision du sort que leur héritage sera partagé, qu’ils soient en grand nombre ou en petit nombre.
57 Waɗannan su ne Lawiyawa da a ƙidaya bisa ga kabilansu, daga Gershom, kabilar Gershonawa; daga Kohat, kabilar Kohatawa; daga Merari, kabilar Merari.
Et ce sont ici les dénombrés de Lévi, selon leurs familles: de Guershon, la famille des Guershonites; de Kehath, la famille des Kehathites; de Merari, la famille des Merarites.
58 Waɗannan kuma su ne kabilan Lawiyawa, kabilar Libniyawa, kabilar Hebronawa, kabilar Maliyawa, kabilar Mushiyawa, kabilar Korayawa (Kohat shi ne kakan Amram;
Ce sont ici les familles de Lévi: la famille des Libnites, la famille des Hébronites, la famille des Makhlites, la famille des Mushites, la famille des Corites. – Et Kehath engendra Amram.
59 sunan matan Amram shi ne Yokebed, ita zuriyar Lawi ce, wadda aka haifa wa Lawiyawa a Masar. A wajen Amram kuwa ta haifi Haruna, Musa da kuma’yar’uwarsu Miriyam.
Et le nom de la femme d’Amram était Jokébed, fille de Lévi, qui naquit à Lévi en Égypte; et elle enfanta à Amram, Aaron et Moïse, et Marie, leur sœur.
60 Haruna shi ne mahaifin Nadab, Abihu, Eleyazar da kuma Itamar.
Et à Aaron naquirent Nadab, et Abihu, Éléazar, et Ithamar.
61 Amma Nadab da Abihu sun mutu sa’ad da suka miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.)
Et Nadab et Abihu moururent comme ils présentaient du feu étranger devant l’Éternel.
62 Dukan’ya’yan Lawiyawa maza daga wata ɗaya zuwa gaba, jimillarsu ta kai 23,000. Ba a ƙidaya su tare da sauran Isra’ilawa ba, domin ba a ba su gādo tare da su ba.
– Et les dénombrés des Lévites furent 23 000, tous les mâles, depuis l’âge d’un mois et au-dessus; car ils ne furent pas dénombrés avec les fils d’Israël, parce qu’on ne leur donna pas d’héritage parmi les fils d’Israël.
63 Waɗannan su ne waɗanda Musa da Eleyazar firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a filaye Mowab kusa da Urdun a hayen Yeriko.
Ce sont là ceux qui furent dénombrés par Moïse et Éléazar, le sacrificateur, qui dénombrèrent les fils d’Israël dans les plaines de Moab, près du Jourdain de Jéricho.
64 Ba ko ɗayansu da yake cikin waɗanda Musa da Haruna firist, suka ƙidaya sa’ad da suka ƙidaya Isra’ilawa a Hamadar Sinai.
Et parmi ceux-là, il n’y en eut aucun de ceux qui avaient été dénombrés par Moïse et Aaron, le sacrificateur, qui dénombrèrent les fils d’Israël dans le désert de Sinaï;
65 Gama Ubangiji ya riga ya gaya wa waɗancan Isra’ilawa cewa lalle za su mutu a hamada, kuma ba ko ɗayansu da ya rage, sai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
car l’Éternel avait dit d’eux: Ils mourront certainement dans le désert; et il n’en resta pas un homme, excepté Caleb, fils de Jephunné, et Josué, fils de Nun.

< Ƙidaya 26 >