< Ƙidaya 21 >

1 Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
When King Arad the Canaanite, which dwelt toward the South, heard tel that Israel came by the way of the spies, then fought hee against Israel, and tooke of them prysoners.
2 Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
So Israel vowed a vowe vnto the Lord, and said, If thou wilt deliuer and giue this people into mine hand, then I wil vtterly destroy their cities.
3 Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
And the Lord heard the voyce of Israel, and deliuered them the Canaanites: and they vtterly destroied them and their cities, and called ye name of the place Hormah.
4 Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
After, they departed from the mount Hor by the way of the red Sea, to compasse the land of Edom: and the people were sore grieued because of the way.
5 suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
And the people spake against God and against Moses, saying, Wherefore haue ye brought vs out of Egypt, to die in the wildernesse? for here is neither bread nor water, and our soule lotheth this light bread.
6 Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
Wherefore the Lord sent fierie serpents among ye people, which stung the people: so that many of the people of Israel died.
7 Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
Therefore the people came to Moses and said, We haue sinned: for wee haue spoken against the Lord, and against thee: pray to the Lord, that he take away the serpents from vs: and Moses prayed for the people.
8 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
And the Lord said vnto Moses, Make thee a fiery serpent, and set it vp for a signe, that as many as are bitten, may looke vpon it, and liue.
9 Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
So Moses made a serpent of brasse, and set it vp for a signe: and when a serpent had bitten a man, then he looked to the serpent of brasse, and liued.
10 Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
And ye children of Israel departed thence, and pitched in Oboth.
11 Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
And they departed from Oboth, and pitched in lie-abarim, in the wildernesse, which is before Moab on the Eastside.
12 Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
They remoued thence, and pitched vpon the riuer of Zared.
13 Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
Thence they departed, and pitched on the other side of Arnon, which is in the wildernesse, and commeth out of the coasts of the Amorites: (for Arnon is the border of Moab, betweene the Moabites and the Amorites)
14 Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
Wherefore it shall be spoken in the booke of the battels of the Lord, what thing he did in the red sea, and in the riuers of Arnon,
15 da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
And at the streame of the riuers that goeth downe to the dwelling of Ar, and lieth vpon the border of Moab.
16 Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
And from thence they turned to Beer: the same is the well where the Lord said vnto Moses, Assemble the people, and I wil giue them water.
17 Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
Then Israel sang this song, Rise vp well, sing ye vnto it.
18 game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
The princes digged this well, the captaines of the people digged it, euen the lawe giuer, with their staues. And from the wildernesse they came to Mattanah,
19 daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
And from Mattanah to Nahaliel, and from Nahaliel to Bamoth,
20 daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
And from Bamoth in the valley, that is in the plaine of Moab, to the top of Pisgah that looketh toward Ieshimon.
21 Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
Then Israel sent messengers vnto Sihon, King of the Amorites, saying,
22 “Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
Let me goe through thy land: we wil not turne aside into the fieldes, nor into the vineyardes, neither drinke of the waters of ye welles: we will goe by the kings way, vntill we be past thy countrey.
23 Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
But Sihon gaue Israel no licence to passe through his countrey, but Sihon assembled all his people, and went out against Israel into the wildernesse: and he came to Iahoz, and fought against Israel.
24 Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
But Israel smote him with the edge of the sword, and conquered his land, from Arnon vnto Iabok, euen vnto ye children of Ammon: for the border of the children of Ammon was strong.
25 Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
And Israel tooke al these cities, and dwelt in all the cities of the Amorites in Heshbon and in all the villages thereof.
26 Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
For Heshbon was the citie of Sihon the king of the Amorites, which had fought beforetime against the king of the Moabites, and had taken al his land out of his hand, euen vnto Arnon.
27 Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
Wherefore they that speake in prouerbes, say, Come to Heshbon, let the citie of Sihon bee built and repaired:
28 “Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
For a fire is gone out of Heshbon, and a flame from the citie of Sihon, and hath consumed Ar of the Moabites, and the lords of Bamoth in Arnon.
29 Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
Wo be to thee, Moab: O people of Chemosh, thou art vndone: he hath suffered his sonnes to be pursued, and his daughters to be in captiuitie to Sihon the king of the Amorites.
30 “Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
Their empire also is lost from Heshbon vnto Dibon, and wee haue destroyed them vnto Nophah, which reacheth vnto Medeba.
31 Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
Thus Israel dwelt in the lande of the Amorites.
32 Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
And Moses sent to searche out Iaazer, and they tooke the townes belonging thereto, and rooted out the Amorites that were there.
33 Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
And they turned and went vp toward Bashan: and Og the King of Bashan came out against them, hee, and all his people, to fight at Edrei.
34 Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
Then the Lord said vnto Moses, Feare him not: for I haue deliuered him into thine hand and all his people, and his land: and thou shalt do to him as thou diddest vnto Sihon the king of the Amorites, which dwelt at Heshbon.
35 Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.
They smote him therefore, and his sonnes, and all his people, vntill there was none left him: so they conquered his land.

< Ƙidaya 21 >