< Ƙidaya 18 >

1 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da’ya’yanka, da kuma iyalin mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi Tentin Sujada, kai da’ya’yanka kaɗai za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.
And Yahweh said unto Aaron, Thou and thy sons and the house of thy father with thee, shall bear the iniquity of the sanctuary, —and, thou, and thy sons with thee, shall bear the iniquity of your priesthood.
2 Ka kawo’yan’uwanka Lawiyawa daga kabilar kakanka tare da kai, don su taimake ka sa’ad da kai da’ya’yanka kuke hidima a gaban Tentin Sujada.
Therefore also thy brethren of the tribe of Levi the stem of thy father, bring thou near with thee, and let them be joined unto thee, and let them wait upon thee, —both on thee and on thy sons with thee, before the tent of the testimony.
3 Za su kasance a ƙarƙashinka, su ne kuma za su yi dukan hidima ta Tenti, amma kada su je kusa da kayayyakin wuri mai tsarki, ko bagade, in ba haka ba, da kai da su, za ku mutu.
So shall they keep thy charge, and the charge of all the tent, —only, unto the vessels of the sanctuary, and unto the altar, shall they not come near, lest they die—both they, and ye.
4 Za su haɗa hannu tare da kai su ɗauki nauyin lura da Tentin Sujada, dukan ayyuka a Tenti, ba kuma wanda zai zo kusa da inda kake.
So shall they be joined unto thee, and shall keep the charge of the tent of meeting, as to all the laborious work of the tent, —but a stranger, shall not come near unto you.
5 “Kai ne za ka ɗauki nauyin lura da wuri mai tsarki da bagade, domin kada fushi yă sāke fāɗa a kan Isra’ilawa.
So shall ye keep the charge of the sanctuary, and the charge of the altar, —that there no more be wrath against the sons of Israel.
6 Ni da kaina na zaɓo’yan’uwanka Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a matsayin kyauta a gare ku, keɓaɓɓu don Ubangiji, domin su yi hidima a Tentin Sujada.
I, therefore, lo! I have taken your brethren the Levites, out of the midst of the sons of Israel, —unto you, as a gift are they given, unto Yahweh, to do the laborious work of the tent of meeting.
7 Amma kai ne kaɗai da’ya’yanka za ku yi aiki a matsayin firistoci game da kowane abu a Tentin Sujada da kuma bayan labule. Ina ba ka aikin firist, yă zama naka. Duk wani kuma da ya zo kusa da wuri mai tsarki, dole a kashe shi.”
But thou and thy sons with thee, shall keep the charge of your priesthood, as to every matter of the altar and as to the interior of the veil, and shall do the laborious work, as a laborious service of gifts, do I give your priesthood, and, the stranger who cometh near shall be put to death.
8 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayun da za a miƙa mini, dukan tsarkakan hadayun da Isra’ilawa suka ba ni, na ba ka su su zama rabonka da na’ya’yanka har abada.
And Yahweh spake unto Aaron, I, therefore, lo! I have given unto thee the charge of my heave-offerings, —as to all the hallowed things of the sons of Israel—unto thee, have I given them. as pertaining to the anointing, and unto thy sons. for a statute age-abiding,
9 Kai za ka riƙe sashe mafi tsarki na hadayun da suka ragu daga wuta. Daga dukan kyautai mafi tsarki na hadayun da suka miƙa mini, ko ta gari, ko don zunubi, ko kuma don laifi, wannan kashi naka ne da’ya’yanka.
This, shall be thine, out of the things most holy, out of the fire, —their every oblation—to the extent of their every meal-offering, and their every sin-bearer, and their every guilt-bearer wherewith they make amends unto me, most holy unto thee, shall it be and unto thy sons.
10 Ku ci shi a matsayin abu mafi tsarki; kowane namiji zai ci. Dole ku ɗauke shi da tsarki.
As something most holy, shall ye eat it, —every male, shall eat it, holy, shall it be unto thee.
11 “Har yanzu kuma duk abin da aka keɓe daga kyautai na dukan hadayun kaɗawa na Isra’ilawa naka ne. Na ba da wannan gare ka da’ya’yanka maza da mata, a kowane lokaci. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
This, therefore, shall be thine—the heave-offering of their gift even all the wave-offerings of the sons of Israel, unto thee, have I given them and unto thy sons and unto thy daughters with thee by a statute age-abiding, —every one that is clean in thy house, shall eat it.
12 “Na ba ka duk man zaitun mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan farinsu da suke bayarwa ga Ubangiji.
All the best of oil, and all the best of new-wine and corn, —the firstfruits thereof which they shall give unto Yahweh, unto thee, have I given them.
13 Dukan nunan fari na ƙasar da suke kawo wa Ubangiji, zai zama naka. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
The firstfruits of all that is in their land which they shall bring in unto Yahweh, thine, shall it be, —every one that is clean in thy house, shall eat it:
14 “Kome a Isra’ila da aka keɓe wa Ubangiji, zai zama naka.
every devoted thing in Israel, thine, shall it be:
15 Kowane haihuwar fari, ta mutum, ko ta dabba da suka miƙa wa Ubangiji, naka ne. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.
every thing that is born first of all flesh that may be offered unto Yahweh among men and among beasts, shall be thine, —only thou shalt, redeem, the firstborn of men, and the firstborn of unclean beasts, shalt thou redeem.
16 Sa’ad da suke wata ɗaya da haihuwa, dole a fanshe su a bakin shekel biyar-biyar, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri da ake amfani da shi, wanda nauyinsa ya kai gera ashirin.
And, as to the redemption price thereof, from a month old, shalt thou redeem, by thine estimate five shekels of silver by the shekel of the sanctuary, —twenty gerahs, it is.
17 “Amma kada ka fanshe ɗan fari na saniya, tunkiya, ko akuya; gama suna da tsarki. Ka yayyafa jininsu a bisan bagade, ka kuma ƙone kitsensu kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Only a firstling ox or a firstling sheep or a firstling goat, shalt thou not redeem, hallowed, they are, —their blood, shalt thou dash against the altar and of their fat, shalt thou make a perfume, an altar-flame, for a satisfying odour unto Yahweh:
18 Namansu zai zama naka, haka ma ƙirji na kaɗawa da cinyar dama za su zama naka.
and their flesh, shall be thine, —as the wave-breast and as the right leg, thine, shall it be:
19 Kome da aka keɓe daga tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da’ya’yanka maza da mata a matsayin zaunannen rabo. Wannan madawwamin alkawarin gishiri ne a gaban Ubangiji dominka da zuriyarka.”
all the heave-offerings of the holy things which the sons of Israel shall heave up unto Yahweh, have I given unto thee and unto thy sons and unto thy daughters with thee by a statute age-abiding, —an age-abiding covenant of salt, it is before Yahweh, for thee and for thy seed with thee.
20 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Ba ka da gādo a ƙasarsu, ba kuwa za ka sami rabo daga cikinsu ba; ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.
Then said Yahweh unto Aaron: In their land, thou shalt have no inheritance, and no allotted portion, shalt thou have in their midst, —I, am thine allotted portion and thine inheritance in the midst of the sons of Israel.
21 “Na ba wa Lawiyawa dukan zakka na Isra’ilawa a matsayin gādonsu, saboda aikin da suke yi yayinda suke hidima a Tentin Sujada.
And unto the sons of Levi, lo! I have given all the tenth in Israel for an inheritance, —the allotted portion for their laborious work which, they are performing, the laborious work of the tent of meeting:
22 Daga yanzu zuwa gaba, kada Isra’ilawa su yi kusa da Tentin Sujada, in ba haka ba kuwa su sha hukuncin zunubinsu, su kuma mutu.
that the sons of Israel come near no more, unto the tent of meeting, —to bear sin, to die.
23 Lawiyawa ne za su yi aikin Tentin Sujada, su kuma ɗauki nauyin kowane laifin da aka aikata a wurin. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce daga yanzu har tsararraki masu zuwa. Ba za su sami gādo a cikin Isra’ilawa ba.
So shall the Levites themselves perform the laborious work of the tent of meeting, and, they, shall bear their iniquity, a statute age-abiding, unto your generations, and in the midst of the sons of Israel, shall they take no inheritance.
24 A maimako haka, na ba wa Lawiyawa zakka da Isra’ilawa suka kawo domin hadaya ga Ubangiji, a matsayin gādonsu. Shi ya sa na ce game da su, ‘Ba su da gādo a cikin Isra’ilawa.’”
Because the tenth of the sons of Israel which they shall offer up unto Yahweh as a heave-offering, have I given unto the Levites as an inheritance, —for this cause, said I regarding them, In the midst of the sons of Israel, shall they take no inheritance.
25 Ubangiji ya ce wa Musa,
Then spake Yahweh unto Moses, saying:
26 “Ka yi wa Lawiyawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka karɓi zakka daga Isra’ila da na ba ku gādo, dole ku miƙa kashi ɗaya bisa goma na wannan zakka a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Unto the Levites, therefore shalt thou speak and shalt say unto them, When ye shall take of the sons of Israel the tenth which I have given unto you from them as your inheritance, then shall ye offer up therefrom the heave-offering of Yahweh, a tenth of the tenth.
27 Za a lissafta hadayarku kamar hatsin da aka sussuka daga masussuka, ko ruwan inabi daga wurin matsewar inabi.
So shall your heave-offering be reckoned your own, —as corn out of the threshing-floor, and as the abundance out of the wine-press.
28 Ta haka za ku miƙa hadaya ga Ubangiji daga cikin dukan zakkar da kuka karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga waɗannan zakka kuwa dole ku ba Haruna firist rabon Ubangiji.
Thus, shall ye also, offer up the heave-offering of Yahweh, out of all your tenths which ye shall take from the sons of Israel, —and give therefrom the heave-offering of Yahweh, unto Aaron the priest.
29 Dole ku miƙa wa Ubangiji rabo mafi kyau da kuma sashi mafi tsarki na kowane abin da aka ba ku.’
Out of all your gifts, shall ye offer up every heave-offering of Yahweh, —out of all the best thereof, the hallowed pert thereof out of it.
30 “Ka faɗa wa Lawiyawa cewa, ‘Sa’ad da kuka miƙa sashi mafi kyau, za a lissafta shi a matsayin abin da ya fito daga masussuka, ko wurin matsewar ruwan inabi ne.
And thou shalt say unto them, —When ye offer the best thereof out of it, then shall it be reckoned to belong unto the Levites, as the increase of the threshing-floor and as the increase of the wine-press,
31 Da kai da gidanka, za ku iya cin abin da ya rage a ko’ina, gama ladan aikinku ne a Tentin Sujada.
And ye shall eat it in any place, ye, and your household, —for a reward, it is unto you, the allotted portion for your laborious work in the tent of meeting.
32 Ta wurin miƙa masa sashi mafi kyau, ba za ku zama masu laifi a wannan batu ba; ta haka ba za ku ƙazantar da tsarkakakkun hadayu na Isra’ilawa ba, ba kuwa za ku mutu ba.’”
And ye shall not by reason of it bear sin, when ye offer up the best thereof, out of it; and the hallowed things of the sons of Israel, shall ye not profane neither shall ye die.

< Ƙidaya 18 >