< Ƙidaya 18 >

1 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da’ya’yanka, da kuma iyalin mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi Tentin Sujada, kai da’ya’yanka kaɗai za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.
And the LORD said unto Aaron, Thou and thy sons and thy fathers’ house with thee shall bear the iniquity of the sanctuary: and thou and thy sons with thee shall bear the iniquity of your priesthood.
2 Ka kawo’yan’uwanka Lawiyawa daga kabilar kakanka tare da kai, don su taimake ka sa’ad da kai da’ya’yanka kuke hidima a gaban Tentin Sujada.
And thy brethren also, the tribe of Levi, the tribe of thy father, bring thou near with thee, that they may be joined unto thee, and minister unto thee: but thou and thy sons with thee shall be before the tent of the testimony.
3 Za su kasance a ƙarƙashinka, su ne kuma za su yi dukan hidima ta Tenti, amma kada su je kusa da kayayyakin wuri mai tsarki, ko bagade, in ba haka ba, da kai da su, za ku mutu.
And they shall keep thy charge, and the charge of all the Tent: only they shall not come nigh unto the vessels of the sanctuary and unto the altar, that they die not, neither they, nor ye.
4 Za su haɗa hannu tare da kai su ɗauki nauyin lura da Tentin Sujada, dukan ayyuka a Tenti, ba kuma wanda zai zo kusa da inda kake.
And they shall be joined unto thee, and keep the charge of the tent of meeting, for all the service of the Tent: and a stranger shall not come nigh unto you.
5 “Kai ne za ka ɗauki nauyin lura da wuri mai tsarki da bagade, domin kada fushi yă sāke fāɗa a kan Isra’ilawa.
And ye shall keep the charge of the sanctuary, and the charge of the altar: that there be wrath no more upon the children of Israel.
6 Ni da kaina na zaɓo’yan’uwanka Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a matsayin kyauta a gare ku, keɓaɓɓu don Ubangiji, domin su yi hidima a Tentin Sujada.
And I, behold, I have taken your brethren the Levites from among the children of Israel: to you they are a gift, given unto the LORD, to do the service of the tent of meeting.
7 Amma kai ne kaɗai da’ya’yanka za ku yi aiki a matsayin firistoci game da kowane abu a Tentin Sujada da kuma bayan labule. Ina ba ka aikin firist, yă zama naka. Duk wani kuma da ya zo kusa da wuri mai tsarki, dole a kashe shi.”
And thou and thy sons with thee shall keep your priesthood for every thing of the altar, and for that within the veil; and ye shall serve: I give you the priesthood as a service of gift: and the stranger that cometh nigh shall be put to death.
8 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayun da za a miƙa mini, dukan tsarkakan hadayun da Isra’ilawa suka ba ni, na ba ka su su zama rabonka da na’ya’yanka har abada.
And the LORD spake unto Aaron, And I, behold, I have given thee the charge of mine heave offerings, even all the hallowed things of the children of Israel, unto thee have I given them by reason of the anointing, and to thy sons, as a due for ever.
9 Kai za ka riƙe sashe mafi tsarki na hadayun da suka ragu daga wuta. Daga dukan kyautai mafi tsarki na hadayun da suka miƙa mini, ko ta gari, ko don zunubi, ko kuma don laifi, wannan kashi naka ne da’ya’yanka.
This shall be thine of the most holy things, [reserved] from the fire: every oblation of theirs, even every meal offering of theirs, and every sin offering of theirs, and every guilt offering of theirs, which they shall render unto me, shall be most holy for thee and for thy sons.
10 Ku ci shi a matsayin abu mafi tsarki; kowane namiji zai ci. Dole ku ɗauke shi da tsarki.
As the most holy things shalt thou eat thereof: every male shall eat thereof; it shall be holy unto thee.
11 “Har yanzu kuma duk abin da aka keɓe daga kyautai na dukan hadayun kaɗawa na Isra’ilawa naka ne. Na ba da wannan gare ka da’ya’yanka maza da mata, a kowane lokaci. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
And this is thine; the heave offering of their gift, even all the wave offerings of the children of Israel: I have given them unto thee, and to thy sons and to thy daughters with thee, as a due for ever: every one that is clean in thy house shall eat thereof.
12 “Na ba ka duk man zaitun mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan farinsu da suke bayarwa ga Ubangiji.
All the best of the oil, and all the best of the vintage, and of the corn, the firstfruits of them which they give unto the LORD, to thee have I given them.
13 Dukan nunan fari na ƙasar da suke kawo wa Ubangiji, zai zama naka. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
The firstripe fruits of all that is in their land, which they bring unto the LORD, shall be thine; every one that is clean in thy house shall eat thereof.
14 “Kome a Isra’ila da aka keɓe wa Ubangiji, zai zama naka.
Every thing devoted in Israel shall be thine.
15 Kowane haihuwar fari, ta mutum, ko ta dabba da suka miƙa wa Ubangiji, naka ne. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.
Every thing that openeth the womb, of all flesh which they offer unto the LORD, both of man and beast, shall be thine: nevertheless the firstborn of man shalt thou surely redeem, and the firstling of unclean beasts shalt thou redeem.
16 Sa’ad da suke wata ɗaya da haihuwa, dole a fanshe su a bakin shekel biyar-biyar, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri da ake amfani da shi, wanda nauyinsa ya kai gera ashirin.
And those that are to be redeemed of them from a month old shalt thou redeem, according to thine estimation, for the money of five shekels, after the shekel of the sanctuary (the same is twenty gerahs).
17 “Amma kada ka fanshe ɗan fari na saniya, tunkiya, ko akuya; gama suna da tsarki. Ka yayyafa jininsu a bisan bagade, ka kuma ƙone kitsensu kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
But the firstling of an ox, or the firstling of a sheep, or the firstling of a goat, thou shalt not redeem; they are holy: thou shalt sprinkle their blood upon the altar, and shalt burn their fat for an offering made by fire, for a sweet savour unto the LORD.
18 Namansu zai zama naka, haka ma ƙirji na kaɗawa da cinyar dama za su zama naka.
And the flesh of them shall be thine, as the wave breast and as the right thigh, it shall be thine.
19 Kome da aka keɓe daga tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da’ya’yanka maza da mata a matsayin zaunannen rabo. Wannan madawwamin alkawarin gishiri ne a gaban Ubangiji dominka da zuriyarka.”
All the heave offerings of the holy things, which the children of Israel offer unto the LORD, have I given thee, and thy sons and thy daughters with thee, as a due for ever: it is a covenant of salt for ever before the LORD unto thee and to thy seed with thee.
20 Ubangiji ya ce wa Haruna, “Ba ka da gādo a ƙasarsu, ba kuwa za ka sami rabo daga cikinsu ba; ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.
And the LORD said unto Aaron, Thou shalt have no inheritance in their land, neither shalt thou have any portion among them: I am thy portion and thine inheritance among the children of Israel.
21 “Na ba wa Lawiyawa dukan zakka na Isra’ilawa a matsayin gādonsu, saboda aikin da suke yi yayinda suke hidima a Tentin Sujada.
And unto the children of Levi, behold, I have given all the tithe in Israel for an inheritance, in return for their service which they serve, even the service of the tent of meeting.
22 Daga yanzu zuwa gaba, kada Isra’ilawa su yi kusa da Tentin Sujada, in ba haka ba kuwa su sha hukuncin zunubinsu, su kuma mutu.
And henceforth the children of Israel shall not come nigh the tent of meeting, lest they bear sin, and die.
23 Lawiyawa ne za su yi aikin Tentin Sujada, su kuma ɗauki nauyin kowane laifin da aka aikata a wurin. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce daga yanzu har tsararraki masu zuwa. Ba za su sami gādo a cikin Isra’ilawa ba.
But the Levites shall do the service of the tent of meeting, and they shall bear their iniquity: it shall be a statute for ever throughout your generations, and among the children of Israel they shall have no inheritance.
24 A maimako haka, na ba wa Lawiyawa zakka da Isra’ilawa suka kawo domin hadaya ga Ubangiji, a matsayin gādonsu. Shi ya sa na ce game da su, ‘Ba su da gādo a cikin Isra’ilawa.’”
For the tithe of the children of Israel, which they offer as an heave offering unto the LORD, I have given to the Levites for an inheritance: therefore I have said unto them, Among the children of Israel they shall have no inheritance.
25 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses, saying,
26 “Ka yi wa Lawiyawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka karɓi zakka daga Isra’ila da na ba ku gādo, dole ku miƙa kashi ɗaya bisa goma na wannan zakka a matsayin hadaya ga Ubangiji.
Moreover thou shalt speak unto the Levites, and say unto them, When ye take of the children of Israel the tithe which I have given you from them for your inheritance, then ye shall offer up an heave offering of it for the LORD, a tithe of the tithe.
27 Za a lissafta hadayarku kamar hatsin da aka sussuka daga masussuka, ko ruwan inabi daga wurin matsewar inabi.
And your heave offering shall be reckoned unto you, as though it were the corn of the threshing-floor, and as the fulness of the winepress.
28 Ta haka za ku miƙa hadaya ga Ubangiji daga cikin dukan zakkar da kuka karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga waɗannan zakka kuwa dole ku ba Haruna firist rabon Ubangiji.
Thus ye also shall offer an heave offering unto the LORD of all your tithes, which ye receive of the children of Israel; and thereof ye shall give the LORD’S heave offering to Aaron the priest.
29 Dole ku miƙa wa Ubangiji rabo mafi kyau da kuma sashi mafi tsarki na kowane abin da aka ba ku.’
Out of all your gifts ye shall offer every heave offering of the LORD, of all the best thereof, even the hallowed part thereof out of it.
30 “Ka faɗa wa Lawiyawa cewa, ‘Sa’ad da kuka miƙa sashi mafi kyau, za a lissafta shi a matsayin abin da ya fito daga masussuka, ko wurin matsewar ruwan inabi ne.
Therefore thou shalt say unto them, When ye heave the best thereof from it, then it shall be counted unto the Levites as the increase of the threshing-floor, and as the increase of the winepress.
31 Da kai da gidanka, za ku iya cin abin da ya rage a ko’ina, gama ladan aikinku ne a Tentin Sujada.
And ye shall eat it in every place, ye and your households: for it is your reward in return for your service in the tent of meeting.
32 Ta wurin miƙa masa sashi mafi kyau, ba za ku zama masu laifi a wannan batu ba; ta haka ba za ku ƙazantar da tsarkakakkun hadayu na Isra’ilawa ba, ba kuwa za ku mutu ba.’”
And ye shall bear no sin by reason of it, when ye have heaved from it the best thereof: and ye shall not profane the holy things of the children of Israel, that ye die not.

< Ƙidaya 18 >