< Ƙidaya 11 >

1 Da Ubangiji ya ji gunagunin da mutanen suke yi saboda wahalarsu, sai ya husata ƙwarai. Sai wuta daga Ubangiji ta yi ta ci a cikinsu har ta ƙone waɗansu wurare na sansanin.
Un notikās, kad tie ļaudis Tā Kunga ausīs kurnēja, tad Tas Kungs to dzirdēja, un Viņa bardzība iekarsa, un Tā Kunga uguns iedegās pret viņiem un rija lēģera galā.
2 Da jama’ar suka yi wa Musa kuka, sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wutar kuwa ta mutu.
Tad tie ļaudis brēca uz Mozu. Un Mozus lūdza To Kungu, un tas uguns noslāpa.
3 Saboda haka aka kira wannan wuri Tabera, gama a wurin ne wuta daga Ubangiji ta ƙuna a cikinsu.
Un tās vietas vārdu nosauca Tabeēra (degums), tāpēc ka Tā Kunga uguns starp tiem bija iededzies.
4 Wata rana, baƙin da suke cikinsu, suka fara kwaɗayin waɗansu abinci, har suka sa Isra’ilawa suka fara kuka, suna cewa, “Da mun sami nama mun ci mana!
Un pulks visādu pienācēju, kas bija viņu starpā, palika kārīgi, un arī Israēla bērni raudāja atkal sacīdami:
5 Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, haka ma kayan lambu irin su kukumba, guna, safa, albasa da kuma tafarnuwa.
Kas mums dos gaļu ēst? Mēs pieminam tās zivis, ko Ēģiptes zemē velti ēdām, gurķus, melones, lokus, sīpolus un ķiplokus.
6 Amma ga shi yanzu ba mu da wani abin marmari; in ba wannan Manna ba!”
Bet nu mūsu dvēsele ir iztvīkusi, jo nav nekā kā vien tas manna priekš mūsu acīm.
7 Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuma kamar ƙaro ne.
Un manna bija tā kā koriandra sēklas un izskatījās kā bdelliums(sveķi).
8 Mutane sukan fita su tattara ta, su niƙa a dutsen niƙa, ko kuwa su daka a turmi. Su dafa, ko su yi waina da ita. Ɗanɗanonta yakan yi kamar abin da aka yi da man zaitun.
Un tie ļaudis skrēja šurp un turp un to sakrāja un mala dzirnavās, vai sagrūda piestās, un to vārīja podos un taisīja no tā raušus, un viņa smaka bija tā kā eļļas raušu smaka.
9 Sa’ad da raɓa tana saukowa da dad dare a kan sansani, Manna ma takan sauko.
Un kad rasa pa naktīm nokrita lēģerī, tad tas manna nokrita līdz.
10 Musa ya ji mutanen suna ta gunaguni ko’ina a cikin iyalansu, kowane mutum a ƙofar tentinsa. Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai, sai Musa ya damu.
Tad Mozus dzirdēja tos ļaudis raudam ar viņu saimēm, ikvienu priekš sava dzīvokļa durvīm, un Tā Kunga bardzība iedegās ļoti, un arī Mozum tas nepatika.
11 Sai ya ce wa Ubangiji, “Me ya sa ka kawo wannan damuwar a kan bawanka? Me na yi da ya ɓata maka rai har ka ɗora dukan nauyin mutanen nan a kaina?
Un Mozus sacīja uz To Kungu: kāpēc Tu Savam kalpam esi darījis tik grūti? Un kāpēc es neesmu atradis Tavās acīs žēlastību, ka Tu man esi uzlicis visu šo ļaužu nastu?
12 Ni ne na yi cikin dukan mutanen nan? Ni ne na haife su? To, me ya sa ka ce in ɗauke su a ƙirjina kamar yadda mai reno yake rungume jariri, zuwa ƙasa wadda ka yi alkawari da rantsuwa za ka ba wa kakanninsu?
Vai es visus šos ļaudis esmu nesis savās miesās? Vai es tos esmu dzemdējis, ka Tu man gribi sacīt: nes tos savā klēpī, tā kā auklētājs nes zīdāmu bērnu, uz to zemi, ko Tu viņu tēviem esi zvērējis?
13 Ina ne zan sami nama in waɗannan mutane? Sun dinga yin mini kuka suna cewa ‘Ka ba mu nama mu ci!’
Kur es gaļas varētu dabūt, ko dot visiem šiem ļaudīm? Jo tie raud pret mani sacīdami: dod mums gaļas ēst.
14 Ba zan iya ɗaukan dukan mutanen nan ni kaɗai ba, nauyin ya yi mini yawa.
Es viens pats visus šos ļaudis nevaru nest, jo tas man ir visai grūti.
15 In haka za ka yi da ni, ka kashe ni yanzu, in na sami tagomashi daga gare ka, kada ka bar ni in rayu in ga wannan baƙin ciki.”
Un ja Tu man tā gribi darīt, tad nokauj labāk mani, ja es žēlastību esmu atradis Tavās acīs, tad neliec man tā redzēt savu nelaimi.
16 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattaro mini dattawa saba’in daga cikin mutanen Isra’ila, waɗanda aka sani su ne dattawa da kuma shugabanni a cikin jama’a. Ka sa su zo Tentin Sujada, su tsaya a can tare da kai.
Un Tas Kungs sacīja uz Mozu: sapulcini Man septiņdesmit vīrus no Israēla vecajiem, kurus tu zini, ka tie ir ļaužu vecaji un viņu virsnieki, un ved Man tos priekš saiešanas telts, un lai tie tur stāv pie tevis;
17 Zan sauko in yi magana da kai a can, zan kuma ɗauki Ruhun da yake kanka in mai da shi wajensu. Za su taimake ka ɗaukan nauyin mutane, don yă zama ba kai kaɗai ba ne mai ɗaukan kaya.
Tad Es nonākšu un ar tevi tur runāšu, un no Tā Gara, kas uz tevis, Es gribu ņemt un likt uz viņiem, un viņiem būs līdz ar tevi nest to ļaužu nastu, ka tā tev vienam nav jānes.
18 “Ka gaya wa mutane, ‘Ku tsarkake kanku don gobe, za ku ci nama. Ubangiji ya ji ku sa’ad da kuka yi kuka cewa, “Da mun sami nama mun ci mana! Ai, da ba mu da damuwa, gama lokacin da muke zama cikin Masar ba mu da damuwa!” Yanzu Ubangiji zai ba ku nama, za ku kuma ci.
Un uz tiem ļaudīm tev būs sacīt: svētījaties uz rīta dienu, tad jūs ēdīsiet gaļu, jo jūs priekš Tā Kunga ausīm esat raudājuši sacīdami: kas mums dos gaļu ēst? Jo mums ir labi klājies Ēģiptes zemē. Tāpēc Tas Kungs jums dos gaļu ēst.
19 Ba za ku ci shi na kwana ɗaya, ko biyu, ko biyar, ko goma, ko kuma kwana ashirin kaɗai ba,
Jūs neēdīsiet vienu nedz divas dienas nedz piecas dienas nedz desmit dienas nedz divdesmit dienas,
20 amma za ku ci har na wata guda cur, sai ya gundure ku a hanci har ku yi ƙyamarsa, domin kun ƙi Ubangiji wanda yake cikinku, kuka yi kuka a gabansa, kuna cewa, “Don me ma muka bar ƙasar Masar?”’”
Bet veselu mēnesi, tiekams tā jums caur nāsīm izies un jūs to apniksiet, tāpēc ka jūs To Kungu esat atmetuši, kas ir jūsu vidū, un priekš Viņa esat raudājuši sacīdami: kāpēc mēs esam izgājuši no Ēģiptes zemes?
21 Amma Musa ya ce, “Ga ni a cikin mutane dubu ɗari shida tafe tare da ni, kana kuma cewa, ‘Zan ba su nama su ci har wata guda cur!’
Un Mozus sacīja: sešsimt tūkstoši ir šo ļaužu kājnieki, kā vidū es esmu, un Tu saki, es tiem došu gaļu, un tiem būs ēst veselu mēnesi!
22 Za su ma sami isashe in har aka yanka musu garkuna tumaki da na shanu? Za su sami isashe in aka kama musu dukan kifin teku?”
Vai tad mazus un lielus lopus priekš tiem būs nokaut, ka tiem būtu diezgan? Jeb vai visas jūras zivis būs sapulcināt, ka tiem būtu diezgan?
23 Ubangiji ya ce wa Musa, “Akwai abin da ya fi ƙarfina ne? Bari ka gani ko abin da na ce zan yi, zai faru ko babu.”
Bet Tas Kungs runāja uz Mozu: vai tad Tā Kunga roka ir paīsināta? Tagad tev būs redzēt, vai Mans Vārds tev notiks, vai ne.
24 Saboda haka Musa ya fita ya gaya wa jama’a abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tattaro dattawansu saba’in, ya sa suka tsaya kewaye da Tentin Sujada.
Un Mozus izgāja un runāja Tā Kunga vārdus uz tiem ļaudīm un sapulcināja septiņdesmit vīrus no to ļaužu vecajiem un nostādīja tos ap saiešanas telti.
25 Sa’an nan Ubangiji ya sauko daga girgije, ya yi magana da shi, ya kuma ɗauke Ruhun da yake kan Musa ya ɗora shi a kan dattawa saba’in nan. Sa’ad da Ruhun ya zauna a kansu, sai suka yi annabci, amma daga wannan ba su ƙara yin haka kuma ba.
Tad Tas Kungs nonāca padebesī un runāja uz to un ņēma no Tā Gara, kas uz viņa bija, un lika to uz tiem septiņdesmit vecajiem, un notikās, kad Tas Gars uz tiem dusēja, tad tie runāja kā pravieši, bet pēc vairs ne.
26 To, fa, akwai dattawa biyu da suka kasance a sansani, wato, Eldad da Medad. Su ma an lasafta su cikin dattawan, amma ba su fita zuwa Tentin Sujada ba. Duk da haka Ruhun ya sauka a kansu, suka kuma yi annabci a cikin sansanin.
Un divi vīri bija palikuši lēģerī, tā viena vārds bija Eldads un tā otra vārds bija Medads, un Tas Gars uz tiem dusēja, jo tie bija starp tiem uzrakstītiem, jebšu nebija nogājuši uz to telti, un tie runāja kā pravieši lēģerī.
27 Wani saurayi ya sheƙa a guje zuwa wajen Musa ya ce, “Eldad da Medad suna can suna annabci a sansani.”
Tad viens puisis tecēja un teica Mozum un sacīja: Eldads un Medads runā lēģerī kā pravieši.
28 Sai Yoshuwa ɗan Nun, wanda yake mataimakin Musa tun yana saurayi, ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, Musa, ka hana su!”
Un Jozuas, Nuna dēls, Mozus sulainis, viens no viņa izlasītiem jaunekļiem, atbildēja un sacīja: mans kungs, Mozu, aizliedz tiem.
29 Amma Musa ya amsa ya ce, “Kana kishi domina ne? Da ma a ce dukan mutanen Ubangiji annabawa ne, da ma a kuma ce Ubangiji ya sa Ruhunsa a kansu mana!”
Tad Mozus uz to sacīja: vai tev deg mani aizstāvēt? Ak kaut Tā Kunga ļaudis visi būtu pravieši un kaut Tas Kungs Savu Garu pār tiem (visiem) dotu!
30 Sai Musa da dattawan Isra’ila suka koma sansani.
Pēc tam Mozus aizgāja atpakaļ lēģerī ar Israēla vecajiem.
31 Ana nan, sai Ubangiji ya kawo wata iska mai tsanani ta koro makware daga teku. Ta bar su birjik kewaye da sansani, tsayinsu daga ƙasa ya kai kamu biyu, misalin tafiyar nisan yini guda ta kowace fuska.
Tad vējš cēlās no Tā Kunga un atveda paipalas no jūras un izkaisīja tās pa lēģeri, šeit vienas dienas gājumu un tur vienas dienas gājumu visapkārt ap lēģeri, un tās bija līdz divām olektīm augstumā pa zemes virsu.
32 Dukan yini da dukan dare da kuma kashegari, mutane suka fito suka tattara makware. Ba wanda ya kāsa tara ƙasa da garwa goma. Sai suka shanya abinsu kewaye da sansanin.
Tad tie ļaudis cēlās cauru dienu un cauru nakti un cauru otru dienu un lasīja paipalas, un kam maz bija, tas bija salasījis desmit gomorus, un tie tās klādami izklāja priekš sevis ap lēģeri.
33 Amma da suna cikin cin naman, tun ba su ma haɗiye ba, sai Ubangiji ya husata sosai a kan jama’ar, ya buge su da annoba mai zafi.
Tā gaļa viņiem vēl bija zobos, pirms tā bija apēsta, tad Tā Kunga bardzība iedegās pret tiem ļaudīm un Tas Kungs sita tos ļaudis ar ļoti grūtu mocību.
34 Saboda haka aka kira wannan wuri Kibrot Hatta’awa, gama a can ne aka binne mutanen nan makwaɗaita.
Tāpēc tās vietas vārdu sauca kārības kapenes, jo tur tie apraka tos kārīgos starp tiem ļaudīm.
35 Daga Kibrot Hatta’awa, mutane suka yi tafiya zuwa Hazerot, a can suka sauka.
No tām kārības kapenēm tie ļaudis aizgāja uz Hacerotu un apmetās Hacerotā.

< Ƙidaya 11 >