< Nehemiya 8 >

1 sai dukan mutane suka taru kamar mutum guda a dandali a gaban Ƙofar Ruwa. Suka faɗa wa Ezra malamin Doka yă fitar da Littafin Dokar Musa, wanda Ubangiji ya umarta domin Isra’ila.
Då nu sjunde månaden kom, och Israels barn voro i sina städer, församlade sig allt folket, såsom en man, på breda gatone inför vattuporten, och sade till Esra den skriftlärda, att han skulle hemta fram Mose lagbok, som Herren Israel budit hade.
2 Saboda haka a rana ta farko ga watan bakwai, Ezra firist, ya kawo Doka a gaban taro, wanda ya ƙunshi maza da mata da dukan waɗanda za su iya fahimta.
Och Esra Presten hemtade fram lagen inför menighetena, både män och qvinnor, och för alla dem som det förstå kunde, på första dagen i sjunde månadenom;
3 Ya karanta Dokar da ƙarfi daga safe har tsakar rana yayinda yake a kan dandali da yake fuskantar dandali a gaban Ƙofar Ruwa, gaban maza, mata da kuma sauran mutanen da za su iya fahimta. Dukan mutane kuwa suka saurara a hankali ga karatun Littafin Dokar.
Och las deruti, på breda gatone, som för vattuporten är, allt ifrå morgonlysningen intill middag, för män och qvinnor, och för dem som det förstå kunde; och hela folkens öron voro vänd till lagbokena.
4 Ezra malamin Doka ya tsaya a kan dakalin itacen da aka yi saboda wannan hidima. Kusa da shi a damansa, Mattitiya, Shema, Anahiya, Uriya, Hilkiya da Ma’asehiya suka tsaya; a hagunsa kuma Fedahiya, Mishayel, Malkiya, Hashum, Hashbaddana, Zakariya da Meshullam suka tsaya.
Och Esra den Skriftlärde stod uppå en hög trästol, den de till predikan gjort hade; och när honom stodo Mattithia, Sema, Anaja, Uria, Hilkia och Maaseja, på hans högra sido; och på hans venstra Pedaja, Misael, Malchija, Hasum, Hasbadana, Zacharia och Mesullam.
5 Sai Ezra ya buɗe littafin. Dukan mutane kuwa suka gan shi domin yana tsaye a bisa fiye da inda mutane suke tsaye; yayinda ya buɗe littafin kuwa, dukan mutane suka miƙe tsaye.
Och Esra lät upp bokena för hela folket; förty han stod högt öfver allt folket; och då han upplät henne, stod allt folket.
6 Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
Och Esra lofvade Herran den stora Guden; och allt folket svarade: Amen, Amen, med uppräckta händer; och bugade sig, och tillbådo Herran med ansigtet ned på jordena.
7 Lawiyawa, wato, su Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma’asehiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan da Felahiya, suka koyar da mutane a cikin Dokar yayinda mutane suke a tsaye a can.
Och Jesua, Bani, Serebia, Jamin, Akkub, Sabbethai, Hodija, Maaseja, Kelita, Asaria, Josabad, Hanan, Pelaja, och Leviterna, beställde att folket gaf akt uppå lagen; och folket stod uppå sitt rum.
8 Suka karanta daga Littafin Dokar Allah, suna sa kowa ya gane, suna kuma ba da fassarar domin mutane su fahimci abin da ake karatu.
Och de läste uti Guds lagbok klarliga och förståndeliga, så att man förstod, då läset vardt.
9 Sa’an nan Nehemiya gwamna, Ezra firist da kuma wanda yake malamin Doka, da Lawiyawa waɗanda suke koyar da mutane, suka ce musu duka, “Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangiji Allahnku. Kada ku yi makoki ko kuka.” Gama dukan mutane suna ta kuka yayinda suke sauraran kalmomin Dokar.
Och Nehemia, hvilken är Thirsatha, och Esra Presten, den Skriftlärde, och Leviterna, som folket höllo till att akta på, sade till allt folket: Denne dagen är helig Herranom edrom Gud; derföre sörjer intet, och gråter icke; ty allt folket gret, då de hörde lagsens ord.
10 Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
Derföre sade han till dem: Går bort, och äter det feta, och dricker det söta, och sänder dem ock delar, som intet för sig tillredt hafva; förty denne dagen är helig vårom Herra. Derföre bekymrer eder icke; ty fröjd i Herranom är edor starkhet.
11 Lawiyawa suka rarrashi mutane duka suna cewa, “Ku natsu, gama wannan rana ce mai tsarki. Kada ku yi baƙin ciki.”
Och Leviterna stillade allt folket, och sade: Varer tyste, ty dagen är helig; bekymrens intet.
12 Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.
Och allt folket gick bort till att äta, dricka och del sända, och gjorde sig en stor glädje; förty de hade förståndit orden, som man dem förkunnat hade.
13 A rana ta biyu ga wata, shugabannin iyalai, tare da firistoci da Lawiyawa, suka taru kewaye da Ezra malamin Doka don su mai da hankali ga kalmomin Dokar.
På annan dagen församlade sig öfversta fäderna ibland allt folket, och Presterna, och Leviterna, till Esra den Skriftlärda, att han skulle undervisa dem i lagsens ordom.
14 Suka tarar a rubuce a cikin Doka wadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa, cewa Isra’ilawa su zauna a bukkoki a lokaci bikin watan bakwai
Och de funno beskrifvet i lagen, att Herren genom Mose budit hade, att Israels barn skulle bo i löfhyddor, på den högtidene i sjunde månadenom.
15 kuma cewa ya kamata su yi shelar wannan magana, su kuma yaɗa ta a duk garuruwansu da kuma cikin Urushalima cewa, “Ku fita zuwa cikin ƙasar tudu ku kawo rassa daga itatuwan zaitun da na zaitun jeji, da kuma daga dargaza, da dabino da itatuwa masu ganye, don yin bukkoki”, kamar yadda yake a rubuce.
Och de läto det varda kunnigt, och utropadt i alla deras städer, och i Jerusalem, och sade: Går ut uppå berget, och hemter oljoqvistar, balsamqvistar, myrthenqvistar, palmqvistar och qvistar af tjockqvistadt trä, att man må göra löfhyddor, såsom skrifvet står.
16 Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
Och folket gick ut, och hemtade, och gjorde sig löfhyddor, hvar uppå sitt tak, och i sina gårdar, och i Guds hus gårdar; och uppå den breda gatone vid vattuporten, och uppå den breda gatone vid Ephraims port.
17 Dukan jama’ar da suka komo daga zaman bauta suka yi bukkoki suka kuma zauna a cikinsu. Daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har yă zuwa yau, Isra’ilawa ba su taɓa yin bikinsa haka ba. Mutane suka cika da farin ciki sosai.
Och hela menigheten af dem, som af fängelset igenkomne voro, gjorde löfhyddor, och bodde deruti; ty Israels barn hade ifrå Josua, Nuns sons, tid, allt intill denna dag, intet så gjort; och var en ganska stor glädje.
18 Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.
Och vardt hvar dag läset i Guds lagbok, ifrå första dagen allt intill den yttersta; och de höllo den högtiden i sju dagar; och på åttonde dagen församlingenes dag, såsom det borde sig.

< Nehemiya 8 >