< Nehemiya 11 >

1 To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
And the princes of the people dwelt in Jerusalem; the rest of the people also cast lots, to bring one of ten to dwell in Jerusalem the holy city, and nine parts in the other cities.
2 Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
And the people blessed all the men that willingly offered themselves to dwell in Jerusalem.
3 Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
Now these are the chiefs of the province that dwelt in Jerusalem; but in the cities of Judah dwelt every one in his possession in their cities, to wit, Israelites, the priests, and the Levites, and the Nethinim, and the children of Solomon's servants.
4 yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
And in Jerusalem dwelt certain of the children of Judah, and of the children of Benjamin. Of the children of Judah: Athaiah the son of Uzziah, the son of Zechariah, the son of Amariah, the son of Shephatiah, the son of Mahalalel, of the children of Perez;
5 da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
and Maaseiah the son of Baruch, the son of Colhozeh, the son of Hazaiah, the son of Adaiah, the son of Joiarib, the son of Zechariah, the son of the Shilonite.
6 Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
All the sons of Perez that dwelt in Jerusalem were four hundred threescore and eight valiant men.
7 Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
And these are the sons of Benjamin: Sallu the son of Meshullam, the son of Joed, the son of Pedaiah, the son of Kolaiah, the son of Maaseiah, the son of Ithiel, the son of Jeshaiah.
8 da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
And after him Gabbai, Sallai, nine hundred twenty and eight.
9 Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
And Joel the son of Zichri was their overseer; and Judah the son of Hassenuah was second over the city.
10 Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
Of the priests: Jedaiah the son of Joiarib, Jachin,
11 da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
Seraiah the son of Hilkiah, the son of Meshullam, the son of Zadok, the son of Meraioth, the son of Ahitub, the ruler of the house of God,
12 tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
and their brethren that did the work of the house, eight hundred twenty and two; and Adaiah the son of Jeroham, the son of Pelaliah, the son of Amzi, the son of Zechariah, the son of Pashhur, the son of Malchijah,
13 da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
and his brethren, chiefs of fathers' houses, two hundred forty and two; and Amashsai the son of Azarel, the son of Ahzai, the son of Meshillemoth, the son of Immer,
14 da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
and their brethren, mighty men of valour, a hundred twenty and eight; and their overseer was Zabdiel, the son of Haggedolim.
15 Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
And of the Levites: Shemaiah the son of Hasshub, the son of Azrikam, the son of Hashabiah, the son of Bunni;
16 da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
and Shabbethai and Jozabad, of the chiefs of the Levites, who had the oversight of the outward business of the house of God;
17 Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
and Mattaniah the son of Mica, the son of Zabdi, the son of Asaph, who was the chief to begin the thanksgiving in prayer, and Bakbukiah, the second among his brethren; and Abda the son of Shammua, the son of Galal, the son of Jeduthun.
18 Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
All the Levites in the holy city were two hundred fourscore and four.
19 Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
Moreover the porters, Akkub, Talmon, and their brethren, that kept watch at the gates, were a hundred seventy and two.
20 Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
And the residue of Israel, of the priests, the Levites, were in all the cities of Judah, every one in his inheritance.
21 Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
But the Nethinim dwelt in Ophel; and Ziha and Gishpa were over the Nethinim.
22 Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
The overseer also of the Levites at Jerusalem was Uzzi the son of Bani, the son of Hashabiah, the son of Mattaniah, the son of Mica, of the sons of Asaph, the singers, over the business of the house of God.
23 Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
For there was a commandment from the king concerning them, and a sure ordinance concerning the singers, as every day required.
24 Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
And Pethahiah the son of Meshezabel, of the children of Zerah the son of Judah, was at the king's hand in all matters concerning the people.
25 Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
And for the villages, with their fields, some of the children of Judah dwelt in Kiriath-arba and the towns thereof, and in Dibon and the towns thereof, and in Jekabzeel and the villages thereof;
26 Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
and in Jeshua, and in Moladah, and Beth-pelet;
27 da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
and in Hazar-shual, and in Beer-sheba and the towns thereof;
28 Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
and in Ziklag, and in Meconah and in the towns thereof;
29 Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
and in En-rimmon, and in Zorah, and in Jarmuth;
30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
Zanoah, Adullam, and their villages, Lachish and the fields thereof, Azekah and the towns thereof. So they encamped from Beer-sheba unto the valley of Hinnom.
31 Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
And the children of Benjamin from Geba onward, at Michmas and Aijah, and at Beth-el and the towns thereof;
32 da Anatot, da Nob, da Ananiya,
at Anathoth, Nob, Ananiah;
33 da Hazor, da Rama, da Gittayim,
Hazor, Ramah, Gittaim;
34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
Hadid, Zeboim, Neballat;
35 da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
Lod, and Ono, Ge-harashim.
36 Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.
And of the Levites, certain courses in Judah were joined to Benjamin.

< Nehemiya 11 >