< Mattiyu 23 >

1 Sa’an nan Yesu ya ce wa taron mutane da kuma almajiransa,
Da talte Jesus til Skarerne og til sine Disciple og sagde:
2 “Malaman dokoki da Farisiyawa suke zama a kujerar Musa.
„Paa Mose Stol sidde de skriftkloge og Farisæerne.
3 Saboda haka dole ku yi musu biyayya, ku kuma yi duk abin da suka faɗa muku. Sai dai kada ku yi abin da suke yi, gama ba sa yin abin da suke wa’azi.
Gører og holder derfor alt, hvad de sige eder; men gører ikke efter deres Gerninger; thi de sige det vel, men gøre det ikke.
4 Sukan ɗaura kaya masu nauyi, su sa wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu, ba sa ko sa yatsa su taimaka.
Men de binde svare Byrder, vanskelige at bære, og lægge dem paa Menneskenes Skuldre; men selv ville de ikke bevæge dem med en Finger.
5 “Kome suke yi, suna yi ne don mutane su gani. Sukan yi layunsufantam-fantam bakin rigunarsu kuma sukan kai har ƙasa;
Men de gøre alle deres Gerninger for at beskues af Menneskene; thi de gøre deres Bederemme brede og Kvasterne paa deres Klæder store.
6 suna son wurin zaman manya a wurin biki, da kuma wuraren zama gaba-gaba a majami’u;
Og de ville gerne sidde øverst til Bords ved Maaltiderne og paa de fornemste Pladser i Synagogerne
7 suna so a yi ta gaisuwarsu a kasuwa, ana kuma riƙa ce musu, ‘Rabbi.’
og lade sig hilse paa Torvene og kaldes Rabbi af Menneskene.
8 “Amma kada a kira ku ‘Rabbi,’ gama kuna da Maigida ɗaya ne, ku duka kuwa,’yan’uwa ne.
Men I skulle ikke lade eder kalde Rabbi; thi een er eders Mester, men I ere alle Brødre.
9 Kada kuma ku kira wani a duniya ‘uba,’ gama kuna da Uba ɗaya ne, yana kuwa a sama.
Og I skulle ikke kalde nogen paa Jorden eders Fader; thi een er eders Fader, han, som er i Himlene.
10 Ba kuwa za a kira ku ‘malam’ ba, gama kuna da Malami ɗaya ne, Kiristi.
Ej heller skulle I lade eder kalde Vejledere; thi een er eders Vejleder, Kristus.
11 Mafi girma a cikinku, zai zama bawanku.
Men den største iblandt eder skal være eders Tjener.
12 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi, duk kuma wanda ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.
Men den, som ophøjer sig selv, skal fornedres, og den, som fornedrer sig selv, skal ophøjes.
13 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, ku munafukai! Kun rufe ƙofar mulkin sama a gaban mutane. Ku kanku ba ku shiga ba, ba kuwa bar waɗanda suke ƙoƙarin shiga su shiga ba.
Men ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I tillukke Himmeriges Rige for Menneskene; thi I gaa ikke derind, og dem, som ville gaa ind, tillade I det ikke.
[Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I opæde Enkers Huse og bede paa Skrømt længe; derfor skulle I faa des haardere Dom.]
15 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi tafiye-tafiye zuwa ƙasashe, ku ƙetare teku don ku sami mai tuba ɗaya, sa’ad da ya tuba kuwa, sai ku mai da shi ɗan wuta fiye da ku, har sau biyu. (Geenna g1067)
Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I drage om til Vands og til Lands for at vinde en eneste Tilhænger; og naar han er bleven det, gøre I ham til et Helvedes Barn, dobbelt saa slemt, som I selv ere. (Geenna g1067)
16 “Kaitonku, makafi jagora! Kukan ce, ‘In wani ya rantse da haikali, ba damuwa; amma in ya rantse da zinariyar haikali, sai rantsuwar ta kama shi.’
Ve eder, I blinde Vejledere! I, som sige: Den, som sværger ved Templet, det er intet; men den, som sværger ved Guldet i Templet, han er forpligtet.
17 Wawaye makafi! Wanne ya fi girma, zinariyar, ko haikalin da yake tsarkake zinariyar?
I Daarer og blinde! hvilket er da størst? Guldet eller Templet, som helliger Guldet?
18 Kukan kuma ce, ‘In wani ya rantse da bagade, ba damuwa; amma in ya rantse da bayarwar da take bisansa, sai rantsuwar ta kama shi.’
Fremdeles: Den, som sværger ved Alteret, det er intet; men den, som sværger ved Gaven derpaa, han er forpligtet.
19 Makafi kawai! Wanne ya fi girma, bayarwar, ko kuwa bagaden da yake tsarkake bayarwar?
I Daarer og blinde! hvilket er da størst? Gaven eller Alteret, som helliger Gaven?
20 Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagade, ya rantse ne da bagaden tare da abin da yake bisansa.
Derfor, den, som sværger ved Alteret, sværger ved det og ved alt det, som er derpaa.
21 Kuma duk wanda ya rantse da haikali, ya rantse ne da shi da kuma wanda yake zaune a cikinsa.
Og den, som sværger ved Templet, sværger ved det og ved ham, som bor deri.
22 Duk kuma wanda ya rantse da sama, ya rantse ne da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune a kansa.
Og den, som sværger ved Himmelen, sværger ved Guds Trone og ved ham, som sidder paa den.
23 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan ba da kashi ɗaya bisa goma na kayan yajinku, na’ana’a, anise, da lafsur. Amma kun ƙyale abubuwan da suka fi girma na dokoki, adalci, jinƙai da aminci. Waɗannan ne ya kamata da kun kiyaye ba tare da kun ƙyale sauran ba.
Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I give Tiende af Mynte og Dild og Kommen og have forsømt de Ting i Loven, der have større Vægt, Retten og Barmhjertigheden og Troskaben. Disse Ting burde man gøre og ikke forsømme hine.
24 Makafi jagora! Kukan tace ƙwaro ɗan mitsil amma sai ku haɗiye raƙumi.
I blinde Vejledere, I, som si Myggen af, men nedsluge Kamelen!
25 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan kwaf da kwano, amma a ciki, cike suke da zalunci da sonkai.
Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I rense det udvendige af Bægeret og Fadet, men indvendigt ere de fulde af Rov og Umættelighed.
26 Kai makaho Bafarisiye! Ka fara wanke cikin kwaf da kwano, sa’an nan bayan ma zai zama da tsabta.
Du blinde Farisæer! rens først det indvendige af Bægeret og Fadet, for at ogsaa det udvendige af dem kan blive rent.
27 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kuna kama da kaburburan da aka shafa musu farin fenti, waɗanda suna da kyan gani a waje, amma a ciki, cike suke da ƙasusuwan matattu da kuma kowane irin abu mai ƙazanta.
Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I ere ligesom kalkede Grave, der jo synes dejlige udvendigt, men indvendigt ere fulde af døde Ben og al Urenhed.
28 Haka ku ma, a waje, a idon mutane, ku masu adalci ne, amma a ciki, cike kuke da munafunci da mugunta.
Saaledes synes ogsaa I vel udvortes retfærdige for Menneskene; men indvortes ere I fulde af Hykleri og Lovløshed.
29 “Kaitonku, malaman dokoki da Farisiyawa, munafukai! Kukan gina kaburbura don annabawa, ku kuma yi wa kaburburan mutane masu adalci ado.
Ve eder, I skriftkloge og Farisæere, I Hyklere! thi I bygge Profeternes Grave og pryde de retfærdiges Gravsteder og sige:
30 Kuna cewa, ‘Da mun kasance a zamanin kakanninmu, ai, da ba mu haɗa hannu da su muka karkashe annabawa ba.’
Havde vi været til i vore Fædres Dage, da havde vi ikke været delagtige med dem i Profeternes Blod.
31 Ta haka kuna ba da shaida a kanku cewa ku zuriyar waɗanda suka karkashe annabawa ne.
Altsaa give I eder selv det Vidnesbyrd, at I ere Sønner af dem, som have ihjelslaaet Profeterne.
32 To, sai ku ci gaba ku cikasa ayyukan da kakanninku suka fara!
Saa gører da ogsaa I eders Fædres Maal fuldt!
33 “Ku macizai!’Ya’yan macizai! Ta yaya za ku tsere wa hukuncin jahannama ta wuta? (Geenna g1067)
I Slanger! I Øgleunger! hvorledes kunne I undfly Helvedes Dom? (Geenna g1067)
34 Saboda haka ina aika muku da annabawa, da masu hikima da malamai. Waɗansunsu za ku kashe ku kuma gicciye; waɗansu kuma za ku yi musu bulala a majami’unku kuna kuma binsu gari-gari.
Derfor se, jeg sender til eder Profeter og vise og skriftkloge; nogle af dem skulle I slaa ihjel og korsfæste, og nogle af dem skulle I hudstryge i eders Synagoger og forfølge fra Stad til Stad,
35 Ta haka alhakin jinin masu adalcin da aka zubar a duniya, tun daga jinin Habila mai adalci, zuwa jinin Zakariya ɗan Berekiya, wanda kuka kashe tsakanin haikali da bagade zai koma kanku.
for at alt det retfærdige Blod skal komme over eder, som er udgydt paa Jorden, fra den retfærdige Abels Blod indtil Sakarias's, Barakias's Søns, Blod, hvem I sloge ihjel imellem Templet og Alteret.
36 Gaskiya nake gaya muku, duk wannan zai auko wa wannan zamani.
Sandelig, siger jeg eder, alt dette skal komme over denne Slægt.
37 “Urushalima, ayya Urushalima, ke da kike kashe annabawa, kike kuma jifan waɗanda aka aiko gare ki, sau da sau na so in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma kuka ƙi.
Jerusalem! Jerusalem! som ihjelslaar Profeterne og stener dem, som ere sendte til dig, hvor ofte vilde jeg samle dine Børn, ligesom en Høne samler sine Kyllinger under Vingerne! Og I vilde ikke.
38 Ga shi, an bar muku gidanku a yashe.
Se, eders Hus lades eder øde!
39 Gama ina gaya muku, ba za ku sāke ganina ba sai kun ce, ‘Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”
Thi jeg siger eder: I skulle ingenlunde se mig fra nu af, indtil I sige: Velsignet være den, som kommer, i Herrens Navn!‟

< Mattiyu 23 >