< Mattiyu 20 >

1 “Mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da sassafe don yă yi hayar mutane su yi aiki a gonar inabinsa.
“For the Kingdom of Heaven is like a man who was the master of a household, who went out early in the morning to hire laborers for his vineyard.
2 Ya yarda yă biya su dinari guda a yini, sai ya tura su gonar inabinsa.
When he had agreed with the laborers for a denarius a day, he sent them into his vineyard.
3 “Wajen sa’a ta uku, ya fita sai ya ga waɗansu suna tsattsaye a bakin kasuwa ba sa kome.
He went out about the third hour, and saw others standing idle in the marketplace.
4 Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi gonar inabina ku yi aiki, zan kuwa biya ku abin da ya dace.’
He said to them, ‘You also go into the vineyard, and whatever is right I will give you.’ So they went their way.
5 Saboda haka suka tafi. “Ya sāke fita a sa’a ta shida da kuma sa’a ta tara, ya sāke yin haka.
Again he went out about the sixth and the ninth hour, and did likewise.
6 Wajen sa’a ta goma sha ɗaya, ya sāke fita, ya tarar da waɗansu har yanzu suna tsattsaye. Ya tambaye su, ‘Don me kuke yini tsattsaye a nan ba kwa kome?’
About the eleventh hour he went out and found others standing idle. He said to them, ‘Why do you stand here all day idle?’
7 “Suka amsa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ “Ya ce musu, ‘Ku ma ku je ku yi aiki a gonar inabina.’
“They said to him, ‘Because no one has hired us.’ “He said to them, ‘You also go into the vineyard, and you will receive whatever is right.’
8 “Sa’ad da yamma ta yi, sai mai gonar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kira ma’aikatan, ka biya su hakkin aikinsu, fara daga waɗanda aka ɗauke su a ƙarshe har zuwa na farko.’
“When evening had come, the lord of the vineyard said to his manager, ‘Call the laborers and pay them their wages, beginning from the last to the first.’
9 “Ma’aikatan da ka ɗauka wajen sa’a ta goma sha ɗaya suka zo, kowannensu kuwa ya karɓi dinari guda.
“When those who were hired at about the eleventh hour came, they each received a denarius.
10 Saboda haka da waɗanda aka ɗauka da fari suka zo, sun zaci za su sami fiye da haka. Amma kowannensu ma ya karɓi dinari guda.
When the first came, they supposed that they would receive more; and they likewise each received a denarius.
11 Sa’ad da suka karɓa, sai suka fara yin gunaguni a kan mai gonar.
When they received it, they murmured against the master of the household,
12 Suna cewa, ‘Waɗannan mutanen da aka ɗauka a ƙarshe sun yi aikin sa’a ɗaya ne kawai, ka kuma mai da su daidai da mu da muka yini muna faman aiki, muka kuma sha zafin rana.’
saying, ‘These last have spent one hour, and you have made them equal to us who have borne the burden of the day and the scorching heat!’
13 “Amma ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Aboki, ban cuce ka ba. Ba ka yarda ka yi aiki a kan dinari guda ba?
“But he answered one of them, ‘Friend, I am doing you no wrong. Didn’t you agree with me for a denarius?
14 Ka karɓi hakkinka ka tafi. Ni na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka.
Take that which is yours, and go your way. It is my desire to give to this last just as much as to you.
15 Ba ni da ikon yin abin da na ga dama da kuɗina ne? Ko kana kishi saboda ni mai kyauta ne?’
Isn’t it lawful for me to do what I want to with what I own? Or is your eye evil, because I am good?’
16 “Saboda haka fa, na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na ƙarshe.”
So the last will be first, and the first last. For many are called, but few are chosen.”
17 To, da Yesu yana haurawa zuwa Urushalima, sai ya ja almajiran nan goma sha biyu gefe, ya ce musu,
As Yeshua was going up to Jerusalem, he took the twelve disciples aside, and on the way he said to them,
18 “Za mu haura zuwa Urushalima, za a kuma bashe Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa
“Behold, we are going up to Jerusalem, and the Son of Man will be delivered to the chief priests and scribes, and they will condemn him to death,
19 za su kuma bashe shi ga Al’ummai su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma a tashe shi!”
and will hand him over to the Gentiles to mock, to scourge, and to crucify; and the third day he will be raised up.”
20 Sai mahaifiyar’ya’yan Zebedin nan ta zo wurin Yesu tare da’ya’yanta, da ta durƙusa a ƙasa, sai ta roƙe shi yă yi mata wani abu.
Then the mother of the sons of Zebedee came to him with her sons, kneeling and asking a certain thing of him.
21 Ya yi tambaya ya ce, “Mene ne kike so?” Ta ce, “Ka sa daga cikin’ya’yan nan nawa biyu, ɗaya yă zauna a damarka, ɗaya kuma a hagunka, a mulkinka.”
He said to her, “What do you want?” She said to him, “Command that these, my two sons, may sit, one on your right hand and one on your left hand, in your Kingdom.”
22 Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?” Suka amsa, “Za mu iya.”
But Yeshua answered, “You don’t know what you are asking. Are you able to drink the cup that I am about to drink, and be immersed with the immersion that I am immersed with?” They said to him, “We are able.”
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce za ku sha daga kwaf na, sai dai zama a damana, ko haguna, ba ni nake da izinin bayarwa ba. Waɗannan wurare na waɗanda Ubana ya shirya wa ne.”
He said to them, “You will indeed drink my cup, and be immersed with the immersion that I am immersed with; but to sit on my right hand and on my left hand is not mine to give, but it is for whom it has been prepared by my Father.”
24 Da goman suka ji haka, sai suka yi fushi da’yan’uwan nan biyu.
When the ten heard it, they were indignant with the two brothers.
25 Yesu ya kira su wuri ɗaya ya ce, “Kun san cewa masu mulkin Al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu kuma sukan gasa musu iko.
But Yeshua summoned them, and said, “You know that the rulers of the nations lord it over them, and their great ones exercise authority over them.
26 Ba haka zai kasance da ku ba. Maimakon haka, duk mai son zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku,
It shall not be so among you; but whoever desires to become great among you shall be your servant.
27 kuma duk mai son zama shugaba, dole yă zama bawanku,
Whoever desires to be first among you shall be your bondservant,
28 kamar yadda Ɗan Mutum bai zo don a bauta masa ba, sai dai don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
even as the Son of Man came not to be served, but to serve, and to give his life as a ransom for many.”
29 Sa’ad da Yesu da almajiransa suke barin Yeriko, sai wani babban taro ya bi shi.
As they went out from Jericho, a great multitude followed him.
30 Makafi biyu kuwa suna zaune a bakin hanya, da suka ji cewa Yesu yana wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
Behold, two blind men sitting by the road, when they heard that Yeshua was passing by, cried out, “Lord, have mercy on us, you son of David!”
31 Mutane suka tsawata musu, suka ce musu su yi shiru. Sai suka ƙara ɗaga murya suna cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
The multitude rebuked them, telling them that they should be quiet, but they cried out even more, “Lord, have mercy on us, you son of David!”
32 Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”
Yeshua stood still and called them, and asked, “What do you want me to do for you?”
33 Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”
They told him, “Lord, that our eyes may be opened.”
34 Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.
Yeshua, being moved with compassion, touched their eyes; and immediately their eyes received their sight, and they followed him.

< Mattiyu 20 >