< Malaki 4 >

1 “Tabbatacce rana tana zuwa; za tă yi ƙuna kamar wutar maƙera. Dukan masu girman kai da kowane mai aikata mugunta zai zama ciyawa, wannan rana mai zuwa za tă ƙone su. Babu saiwa ko reshen da za a bar musu,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Porque eis que aquele dia vem ardendo como o forno: todos os soberbos, e todos os que obram a impiedade, serão como a palha; e o dia que está para vir os abrazará, diz o Senhor dos exércitos, de sorte que lhes não deixará nem raiz nem ramo
2 Amma ku da kuke girmama sunana, ranar adalci za tă fito tare da warkarwa a fikafikanta. Za ku kuwa fita kuna tsalle kamar’yan maruƙan da aka sake daga garke.
Mas a vós, que temeis o meu nome, nascerá o sol da justiça, e saúde trará debaixo das suas asas; e saireis, e crescereis como os bezerros do cevadouro.
3 Sa’an nan za ku tattake mugaye; za su zama toka a ƙarƙashin tafin ƙafafunku a ranar da zan aikata waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
E pizareis os ímpios, porque se farão cinza debaixo das plantas de vossos pés, no dia em que fizer isto, diz o Senhor dos exércitos.
4 “Ku tuna da dokar bawana Musa, ƙa’idodi da dokokin da na ba shi a Horeb domin dukan Isra’ila.
Lembrai-vos da lei de Moisés, meu servo, que lhe mandei em Horeb para todo o Israel, dos estatutos e juízos.
5 “Ga shi, zan aika muku da annabi Iliya kafin babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji tă zo.
Eis que eu vos envio o profeta Elias, antes que venha o dia grande e terrível do Senhor;
6 Zai juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, zukatan’ya’ya kuma ga iyayensu; in ba haka ba zan bugi ƙasar da hallaka gaba ɗaya.”
E converterá o coração dos pais aos filhos, e o coração dos filhos a seus pais; para que eu não venha, e fira a terra com maldição.

< Malaki 4 >