< Malaki 1 >

1 Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
Tā Kunga vārda spriedums par Israēli caur Malahiju.
2 “Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
Es jūs esmu mīlējis, saka Tas Kungs; bet jūs sakāt: kā Tu mūs esi mīlējis? Vai Ēsavs nav Jēkabam brālis? Saka Tas Kungs; tomēr Es Jēkabu mīlēju
3 amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
Un Ēsavu Es ienīdēju un viņa kalnus darīju par posta vietu un viņa mantas tiesu priekš šakāļiem tuksnesī.
4 Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
Un jebšu Edoms sacītu: mēs esam salauzti, tomēr tās posta vietas atkal gribam uztaisīt, - tad Tas Kungs Cebaot saka tā: tie uztaisīs, bet Es noārdīšu, un tos nosauks par bezdievības robežām un par ļaudīm, par ko Tas Kungs mūžīgi dusmo.
5 Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
Un jūsu acis to redzēs, un jūs sacīsiet: Tas Kungs pagodināsies pāri pār Israēla robežām. -
6 “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
Dēlam būs godāt savu tēvu, un kalpam savu kungu. Ja Es esmu Tēvs, kur ir Mans gods? Un ja Es esmu Kungs, kur ir Mana bijāšana? saka Tas Kungs Cebaot uz jums priesteriem, Mana Vārda nicinātajiem; bet jūs sakāt: kā tad mēs nicinājam Tavu Vārdu?
7 “Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
Jūs nesat uz Manu altāri sagānītu maizi. Tad jūs sakāt: ar ko mēs Tevi sagānījām? Ar to, ka jūs sakāt: Tā Kunga galds nav cienījams.
8 Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Jo kad jūs ko aklu atnesat upurēt, tad tas jums nav nelabs, un ja jūs ko tizlu vai vāju atnesat, tad tas nav nelabs. Atnesat to jel savam valdītājam, vai viņam pie tevis būs labs prāts, jeb vai viņš tavu vaigu žēlīgi uzlūkos? saka Tas Kungs Cebaot.
9 “To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Nu tad pielūdziet jel Dieva vaigu, lai Viņš mums ir žēlīgs. No jūsu rokas tas noticis: vai tad Viņš jūsu vaigu žēlīgi uzskatīs? saka Tas Kungs Cebaot.
10 “Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Kaut jel kāds būtu jūsu starpā, kas durvis aizslēdz, lai jūs velti uguni neiededzinājāt uz Mana altāra; Man nav labs prāts pie jums, saka Tas Kungs Cebaot, un tas upuris no jūsu rokām Man nepatīk.
11 Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Jo no saules uzlēkšanas līdz noiešanai Mans Vārds ir paaugstināts starp tautām, un ikkatrā vietā Manam Vārdam top kvēpināts un šķīsts upuris atnests. Jo Mans Vārds ir liels starp tautām, saka Tas Kungs Cebaot.
12 “Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
Bet jūs to sagānat, sacīdami: Tā Kunga galds, tas ir sagānīts, un viņa ienākumu riebj baudīt.
13 Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
Un jūs sakāt: redzi, kāds grūtums! Un nebēdājat par to, saka Tas Kungs Cebaot, jūs atnesat, kas ir laupīts, un kas tizls un vājš, un tā upurējat upuri. Vai tas Man var patikt no jūsu rokas? saka Tas Kungs.
14 “La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Nolādēts tas blēdis, kam savā ganāma pulkā ir auniņš, un kas sola un upurē Tam Kungam ko maitātu! Jo Es esmu liels Ķēniņš, saka Tas Kungs Cebaot: un Mans Vārds ir bijājams starp tautām.

< Malaki 1 >