< Malaki 1 >

1 Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
K A WANANA o ka olelo a Iehova i ka Iseraela ma o Malaki la.
2 “Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
Ua aloha aku au ia oukou, wahi a Iehova; Aka, ke ninau mai nei oukou, Ma ke aha la kau i aloha mai ai ia makou? Aole anei o Esau ka hoahanau o Iakoba? wahi a Iehova; Aka, i aloha aku au ia Iakoba,
3 amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
A hoowahawaha hoi au ia Esau, A hooneoneo aku la au i kona mau mauna, A hoolilo iho la i kona aina i mau wahi noho o ka waonahele.
4 Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
No ka mea, ke olelo nei ko Edoma, Ua auhulihia kakou, Aka, e kukulu hou auanei kakou i na wahi neoneo: Penei ka Iehova o na kaua i olelo mai ai, E kukulu lakou, a e wawahi hoi au: E kapaia lakou, Na aina o ka aia, A o na kanaka a Iehova e inaina mau loa ai.
5 Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
A e ike auanei ko oukou mau maka, a e olelo aku oukou, E hoonuiia auanei o Iehova mai ka palena aku o Iseraela.
6 “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
Ua hoomaikai ke keiki i kona makuakane, A o ke kauwa i kona haku: Ina hoi he makua wau, auhea la kuu hoomaikaiia? Ina hoi he haku wau, auhea la hoi kuu weliweliia? Wahi a Iehova o na kaua ia oukou, e na kahuna hoowahawaha i kuu inoa. Ke ninau mai nei oukou, Ma ke aha ka makou i hoowahawaha ai i kou inoa?
7 “Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
Ke mohai mai nei oukou i ka berena haumia maluna o ko'u kuahu; Ke ninau mai nei oukou, Ma ke aha la ka makou i hoohaumia aku ai ia oe? Ma ka mea a oukou e olelo nei, He mea wahawaha ka papaaina o Iehova.
8 Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Ina paha e kaumaha oukou i ka mea makapo i mea mohai, aole anei ia he hewa? Ina hoi e mohai oukou i ka mea oopa a me ka mea mai, aole anei he hewa ia? Ke i aku nei au, e haawi aku ia mea na kou alii, E oluolu mai anei ia ia oe? E maliu mai anei kela ia oe? wahi a Iehova o na kaua.
9 “To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
Nolaila hoi, ke nonoi aku nei oukou i ke Akua, e aloha mai oia ia kakou: No oukou aku ia mea; e maliu mai anei kela ia oukou? Wahi a Iehova o na kaua.
10 “Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Owai la ka mea o oukou e pani wale i na puka? Aole oukou e kuni make hewa maluna o kuu kuahu. Aole au i oluolu ia oukou, wahi a Iehova o na kaua; Aole hoi e maliu au i ka mohai na ko oukou lima mai.
11 Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
No ka mea, mai ka hikina o ka la a hiki i ke komohana, E nui auanei kuu inoa iwaena o na lahuikanaka; A ma na wahi a pau loa e kuniia'i ka mea ala no kuu inoa, A me ka mohai maemae: No ka mea, e nui auanei kuu inoa iwaena o na lahuikanaka, Wahi a Iehova o na kaua.
12 “Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
Aka, ua hoino oukou ia i ka oukou olelo ana, Ua haumia ka papaaina o Iehova, A o ka hua maluna, oia o kana ai, he mea hoowahawaha ia.
13 Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
Ke olelo nei oukou, Ka! kai ka luhi! A na oukou ia i hoopailuaia'i, wahi a Iehova o na kaua; No ka mea, ke mohai iho nei oukou i ka mea i haehaeia, A me ka oopa, a me ka maimai, A pela oukou i lawe mai ai i ka mohai. E oluolu anei au i keia mea na ko oukou lima mai? wahi a Iehova.
14 “La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Aka, auwe ka mea hoopunipuni, Ka mea nana ka hipakane maloko o kana ohana, Aka, ua hoolaa, a ua mohai iho i ka mea haumia: No ka mea, he alii nui hoi wau, wahi a Iehova o na kaua, A he mea weliweli ko'u inoa iwaena o na lahuikanaka.

< Malaki 1 >