< Luka 23 >

1 Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
Then they all rose in a body and led Jesus before Pilate.
2 Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
And they began to accuse him, ‘This is a man whom we found misleading our people, preventing them from paying taxes to the Emperor, and giving out that he himself is “Christ, a king.”’
3 Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
‘Are you the king of the Jews?’ Pilate asked him. ‘It is true,’ replied Jesus.
4 Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
But Pilate, turning to the chief priests and the people, said, ‘I do not see anything to find fault with in this man.’
5 Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
But they insisted, ‘He is stirring up the people by his teaching all through Judea; he began with Galilee and has now come here.’
6 Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
Hearing this, Pilate asked if the man was a Galilean;
7 Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
and, having satisfied himself that Jesus came under Herod’s jurisdiction, he sent him to Herod, who also was at Jerusalem at the time.
8 Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
When Herod saw Jesus, he was exceedingly pleased, for he had been wanting to see him for a long time, having heard a great deal about him; and he was hoping to see some sign given by him.
9 Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.
So he questioned him at some length, but Jesus made no reply.
10 Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
Meanwhile the chief priests and the teachers of the Law stood by and vehemently accused him.
11 Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
And Herod, with his soldiers, treated Jesus with scorn; he mocked him by throwing a gorgeous robe round him, and then sent him back to Pilate.
12 A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
And Herod and Pilate became friends that very day, for before that there had been ill-will between them.
13 Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
So Pilate summoned the chief priests, and the leading men, and the people,
14 ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
and said to them, ‘You brought this man before me charged with misleading the people; and yet, for my part, though I examined him before you, I did not find this man to blame for any of the things of which you accuse him;
15 Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
nor did Herod either; for he has sent him back to us. And, as a fact, he has not done anything deserving death;
16 Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
so I will have him scourged, and then release him.’
18 Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
But they began to shout as one man, ‘Kill this fellow, but release Barabbas for us.’
19 (Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
(Barabbas was a man who had been put in prison for a riot that had broken out in the city and for murder.)
20 Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
Pilate, however, wanting to release Jesus, called to them again;
21 Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
but they kept calling out, ‘Crucify, crucify him!’
22 Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
‘Why, what harm has this man done?’ Pilate said to them for the third time. ‘I have found nothing in him for which he could be condemned to death. So I will have him scourged, and then release him.’
23 Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
But they persisted in loudly demanding his crucifixion; and their clamour gained the day.
24 Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
Pilate decided that their demand should be granted.
25 Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
He released the man who had been put in prison for riot and murder, as they demanded, and gave Jesus up to be dealt with as they pleased.
26 Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
And, as they were leading Jesus away, they laid hold of Simon from Cyrene, who was on his way in from the country, and they put the cross on his shoulders, for him to carry it behind Jesus.
27 Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
There was a great crowd of people following him, many being women who were beating their breasts and wailing for him.
28 Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda’ya’yanku.
So Jesus turned and said to them, ‘Women of Jerusalem, do not weep for me, but weep for yourselves and for your children.
29 Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
A time, I tell you, is coming, when it will be said – “Happy are the women who are barren, and those who have never borne children or nursed them!”
30 Sa’an nan “‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!”’
At that time people will begin to say to the mountains “Fall on us,” and to the hills “Cover us.”
31 Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
If what you see is done while the tree is green, what will happen when it is dry?’
32 Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
There were two others also, criminals, led out to be executed with Jesus.
33 Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
When they had reached the place called “The Skull,” there they crucified Jesus and the criminals, one on the right, and one on the left.
34 Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.
Then Jesus said, ‘Father, forgive them; they do not know what they are doing.’ His clothes they divided among them by casting lots.
35 Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
Meanwhile the people stood looking on. Even the leading men said with a sneer, ‘He saved others, let him save himself, if he is God’s Christ, his chosen one.’
36 Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
The soldiers, too, came up in mockery, bringing him common wine,
37 Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
and saying as they did so, ‘If you are the king of the Jews, save yourself.’
38 Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
Above him were the words – “THIS IS THE KING OF THE JEWS.”
39 Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
One of the criminals who were hanging beside Jesus railed at him. ‘Aren’t you the Christ? Save yourself and us,’ he said.
40 Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
But the other rebuked him. ‘Haven’t you,’ he said, ‘any fear of God, now that you are under the same sentence?
41 Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
And we justly so, for we are only reaping our deserts, but this man has not done anything wrong.
42 Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
Jesus,’ he went on, ‘do not forget me when you have come to your kingdom.’
43 Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
And Jesus answered, ‘I tell you, this very day you will be with me in Paradise.’
44 Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
It was nearly midday, when a darkness came over the whole country, lasting until three in the afternoon,
45 domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
the sun being eclipsed; and the Temple curtain was torn down the middle.
46 Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
Then Jesus, with a loud cry, said, ‘Father, into your hands I commit my spirit.’ And with these words he expired.
47 Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
The Roman centurion, on seeing what had happened, praised God, exclaiming, ‘This must have been a good man!’
48 Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
All the people who had collected to see the sight watched what occurred, and then went home beating their breasts.
49 Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
All the friends of Jesus had been standing at a distance, with the women who accompanied him from Galilee, watching all this.
50 Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
Now there was a man of the name of Joseph, who was a member of the Council, and who bore a good and upright character.
51 shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
(This man had not assented to the decision and action of the Council.) He belonged to Arimathea, a town in Judea, and lived in expectation of the kingdom of God.
52 Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
He now went to see Pilate, and asked for the body of Jesus;
53 Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
and, when he had taken it down, he wrapped it in a linen sheet, and laid him in a tomb cut out of stone, in which no one had yet been buried.
54 An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
It was the Preparation day, and just before the Sabbath began.
55 Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
The women who had accompanied Jesus from Galilee followed, and saw the tomb and how the body of Jesus was laid,
56 Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.
and then went home, and prepared spices and perfumes. During the Sabbath they rested, as directed by the commandment.

< Luka 23 >