< Luka 16 >

1 Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
Then He said further to His disciples: “There was a certain rich man who had a manager, who was accused to him of wasting his goods.
2 Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
So he called him in and said to him: ‘What is this I hear about you? Render an account of your stewardship, because you can no longer be manager.’
3 “Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
Then the manager said within himself: ‘What shall I do? My master is taking the management away from me. I do not have strength to dig; I am ashamed to beg
4 Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
—I know what I will do, so that whenever I am removed from the management they may receive me into their houses.’
5 “Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
Summoning each one of his master's debtors, he said to the first, ‘How much do you owe my master?’
6 “Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
And he said, ‘A hundred baths of olive oil.’ So he said to him, ‘Take your bill and sit down quickly and write fifty.’
7 “Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
Then he said to another, ‘And how much do you owe?’ And he said, ‘A hundred measures of wheat.’ So he said to him, ‘Take your bill and write eighty.’
8 “Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
The master even ‘commended’ the dishonest manager, because he had acted shrewdly. The sons of this age are shrewder in their own generation than the sons of the Light. (aiōn g165)
9 Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
“I even say to you, make friends for yourselves by means of unrighteous mammon, so that whenever you fail, they may receive you into the eternal dwellings! (aiōnios g166)
10 “Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
He who is faithful in a very little is faithful also in much, and he who is dishonest in a very little is dishonest also in much.
11 In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
If therefore you have not been faithful with the unrighteous mammon, who will commit to your trust the genuine?
12 In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
And if you have not been faithful in what belongs to another, who will give you what is your own?
13 “Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
No servant can serve two masters; either he will hate the one and love the other, or he will be devoted to the one and despise the other. You cannot serve God and mammon!”
14 Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
Now the Pharisees, who were lovers of money, were also listening to all these things, and they were ridiculing Him.
15 Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
So He said to them: “You are those who justify yourselves before men, but God knows your hearts. That which is exalted among men is an abomination before God.
16 “An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
The Law and the Prophets were until John; since then the Kingdom of God is being proclaimed, and every one is trying to force his way into it.
17 Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
But it is easier for heaven and earth to pass away, than for one tittle of the Law to fail.
18 “Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
“Whoever divorces his wife and marries another woman commits adultery, and whoever marries her who is divorced from her husband commits adultery.
19 “An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
“Now there was a certain rich man who was dressed in purple and fine linen, living in luxury every day.
20 A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
And there was a certain beggar named Lazarus, covered with sores, who had been placed at his gate,
21 Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
just wanting to be fed with the crumbs that fell from the rich man's table—why even the dogs would come and lick his sores!
22 “Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
In due time the beggar died and was carried away to Abraham's bosom by the angels. “The rich man also died and was buried.
23 A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
And in Hades he looked up and saw Abraham at a distance, and Lazarus very close to him. And being in torment, (Hadēs g86)
24 Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
he called out, saying, ‘Father Abraham, have mercy on me and send Lazarus, that he may dip the tip of his finger in water and cool my tongue; because I am tormented by this flame!’
25 “Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
But Abraham said: ‘Child, remember that in your lifetime you received your good things, while Lazarus had bad things; but now he is being comforted, and you tormented.
26 Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
And besides all this, between us and you a great chasm has been fixed, so that those who want to pass from here to you cannot, nor can anyone from there cross over to us.’
27 “Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
Then he said, ‘I beg you therefore, father, that you would send him to my father's house,
28 gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
because I have five brothers, so that he may testify to them, lest they also come to this place of torment.’
29 “Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
Abraham said to him, ‘They have Moses and the prophets; let them hear them.’
30 “Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
So he said to him, ‘Oh no, father Abraham—if someone from the dead should go to them, they will repent!’
31 “Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”
He said to him, ‘If they do not listen to Moses and the prophets, they will not be persuaded even if someone should rise from the dead.’”

< Luka 16 >