< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Ko so mnogi jeli opisovati rečí, ktere so popolnoma gotove med nami,
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
Kakor so nam izročili, kteri so od začetka sami videli in so služabniki besede bili:
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
Namenil sem tudi jaz, ki sem vse od začetka na tanko pozvedel, po vrsti pisati tebi, častiti Teofil!
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
Da spoznaš gotovost rečî, kterih si se naučil.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
Bil je v dnéh Heroda kralja Judejskega neki duhoven po imenu Zaharija, od reda Abijevega; in žena njegova od hčeri Aronovih, in ime jej je bilo Elizabeta.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
Bila sta pa oba pravična pred Bogom, in živela sta po vseh zapovedih in ustavah Gospodovih brez madeža.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
In nista imela otrók, ker je bila Elizabeta nerodovitna, in oba sta se bila uže postarala.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
Zgodí se pa, ko je po vrsti reda svojega služil pred Bogom,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
Po navadi duhovstva zadene ga opravilo, naj vnide v tempelj Gospodov, da pokadí.
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
In vsa množiča ljudstva je bila zunej, in molila je v čas kajenja.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
Prikaže pa mu se angelj Gospodov, stoječ na desnej strani kadilnega oltarja.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
In Zaharija se ustraši, ko ga ugleda, in groza ga obide.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
Angelj mu pa reče: Ne boj se, Zaharija! kajti uslišana je molitev tvoja, in žena tvoja Elizabeta ti bo rodila sina, in imenuj ime njegovo Janez.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
In bo ti na radost in na veselje, in veliko se jih bo rojstvu njegovemu radovalo.
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
Kajti velik bo pred Gospodom; in vina in močne pijače ne bo pil, in napolnil se bo Duha svetega še v telesu matere svoje.
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
In veliko sinov Izraelskih bo obrnil h Gospodu Bogu njih.
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
In on pojde pred njim z duhom in močjó Elijevo, da obrne srca očetov k otrokom, in nevernike k razumnosti pravičnih: da pripravi Gospodu ljudstvo gotovo.
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
Pa reče Zaharija angelju: Po čem bom poznal to? kajti jaz sem star, in žena moja se je postarala.
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
In odgovarjajoč angelj, reče mu: Jaz sem Gabrijel, ki stojim pred Bogom, in poslan sem, naj s teboj govorim, in ti to veselje oznanim.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
In glej, mutast boš in ne boš mogel govoriti do dné, ko se bo to zgodilo; ker nisi veroval besedam mojim, ktere se bodo izpolnile o svojem času.
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
In čakalo je ljudstvo Zaharija; in čudili so se, da se tako dolgo mudí v tempeljnu.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
Ko pa izide, ni jim mogel govoriti? in spoznajo, da je videl prikazen v tempeljnu: in on jim je pomigaval, in ostal je mutast.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
In zgodí se, ko se izpolnijo dnevi službe njegove, odide na dom svoj.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
A po teh dnéh je Elizabeta žena njegova spočela, in skrivala se je pet mesecev, govoreč:
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
Tako mi je storil Gospod v dnéh, ko se je ozrl na me, da odvzeme oponos moj med ljudmí.
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
A šesti mesec pošlje Bog angelja Gabrijela v mesto Galilejsko, kteremu je ime Nazaret,
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
K devici zaročenej možu, kteremu je bilo ime Jožef, iz hiše Davidove; in devici je bilo ime Marija.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
In angelj vnide k njej, in reče: Zdrava, z milostjo obdarovana! Gospod je s teboj; blagoslovljena si ti med ženami.
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
Ona pa, ko ga ugleda, prestraši se od besede njegove, in premišljevala je, kakošen bi bil ta pozdrav.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
Pa jej angelj reče; Ne boj se, Marija! našla si namreč milost pri Bogu.
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
In glej, spočela boš v telesu, in rodila boš sina, in imenuj ime njegovo Jezus.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
Ta bo velik, in imenoval se bo sin najvišega; in dal mu bo Gospod Bog prestol Davida očeta njegovega,
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
In kraljeval bo v hiši Jakobovej vekomaj, in kraljestvu njegovemu ne bo konca. (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
Marija pa reče angelju: Kako bo to, ko moža ne poznam?
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
In odgovarjajoč angelj, reče jej; Sveti Duh bo prišel na te, in moč najvišega te bo obsenčila; za to se bo sveto, ktero se bo rodilo iz tebe, imenovalo sin Božji.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
In glej, Elizabeta teta tvoja, tudi ona je spočela sina v starosti svojej; in ta mesec jej je šesti, njej, ki jo imenujejo nerodovitno:
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
Ker ne bo nobene besede pri Bogu, ktera se ne bi mogla izpolniti.
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
Marija pa reče: Glej, dekla sem Gospodova; zgôdi mi se po besedi tvojej. In angelj odide od nje.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
Vstavši pa Marija v té dni, odide jadrno na gorenjo stran v mesto Judovo.
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
In vnide v hišo Zaharijevo, in pozdravi Elizabeto.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
In zgodí se, ko sliši Elizabeta pozdrav Marijin, zaigra dete v telesu njenem; in Elizabeta se napolni Duha svetega,
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
In zavpije z močnim glasom, in reče: Blagoslovljena si ti med ženami, in blagoslovljen je sad telesa tvojega.
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
In odkod meni to, da je prišla mati Gospoda mojega k meni?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
Kajti glej, ko je prišel glas pozdrava tvojega v ušesa moja, zaigralo je dete radostno v telesu mojem.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
In blagor jej, ktera je verovala; kajti zgodilo se bo, kar jej je rekel Gospod.
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
Pa reče Marija: Duša moja poveličuje Gospoda,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
In duh moj se je oveselil v Bogu, zveličarji mojem:
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
Da se je ozrl na ponižanje dekle svoje. Kajti glej, odslej me bodo blagrovali vsi rodovi:
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
Ker mi je storil velike rečí on, ki je mogočen, in ime njegovo sveto;
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
In usmiljenje njegovo od roda do roda tistim, kteri se ga bojé.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
Pokazal je moč z roko svojo: razkropil je ošabne v mislih srca njih;
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
Vrgel je mogočne s prestola, in povišal je ponižne.
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
Lačne je napolnil z blagom, in bogate je odpravil prazne.
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
Sprejel je Izraela hlapca svojega, da se spomene usmiljenja svojega.
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
(Kakor je govoril očetom našim, ) Abrahamu in semenu njegovemu na vekomaj. (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
Prebila je pa Marija ž njo kake tri mesece; in vrne se na dom svoj.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
A Elizabeti se izpolni čas, da porodí, in rodí sina.
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
In sosedje in sorodniki njeni zaslišijo, da je pokazal Gospod veliko usmiljenje svoje na njej; in radovali so se ž njo.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
In zgodí se osmi dan, da pridejo deteta obrezovat; in klicali so ga po imenu očeta njegovega, Zaharija.
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
Ali odgovarjajoč mati njegova, reče: Ne, nego imenoval se bo Janez.
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
In rekó jej: Nikogar ni v rodovini tvojej, da bi mu bilo tako ime.
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
In pomigavali so očetu njegovemu, kako hoče, da bi ga imenovali.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
In izprosivši tablico, napiše, govoreč: Janez mu je ime. In vsi se začudijo.
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
In odprla so se usta njegova pri tej priči in jezik njegov, in govoril je, hvaleč Boga.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
In strah obide vse njih sosede; in po vsej gorenjej Judeji se razglasé vse te reči.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
In vsi, kteri jih slišijo, položé jih v srce svoje, govoreč: Kaj neki bo iz tega otroka? In roka Gospodova je bila ž njim.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
In Zaharija oče njegov se napolni Duha svetega, in prerokuje, govoreč:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
Blagoslovljen Gospod Bog Izraelov, da je obiskal in odrešil ljudstvo svoje;
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
In nam povzdignil rog zveličanja v hiši Davida hlapca svojega,
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
(Kakor je govoril z ustmi svetih prerokov svojih, ki so bili od nekedaj: ) (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
Da nas bo rešil sovražnikov naših in iz rok vseh, kteri nas mrzé:
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
Da storí usmiljenje očetom našim, in se spomene svete zaveze svoje,
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
Prisege, ktero je prisegel Abrahamu očetu našemu, da nam bo dal,
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
Da mu, rešeni iz rok sovražnikov svojih, brez straha služimo,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
V svetosti in pravičnosti pred njim vse svoje žive dní.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
In ti, otrok, imenoval se boš prerok najvišega; kajti šel boš pred obličjem Gospodovim, da mu pripraviš pot;
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
In daš razum zveličanja ljudstvu njegovemu za odpuščanje njih grehov,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
Po prisrčnem usmiljenji Boga našega, po kterem nas je obiskal vzhod z vižave:
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
Da obsije tiste, kteri sedé v temi in smrtnej senci; da naravná noge naše na pot mirú.
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
A dete je rastlo in se krepčalo v duhu; in bilo je v puščavah do dné, ko se pokaže Izraelu.

< Luka 1 >