< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
如你所知,很多人都曾试图用文字记录我们参与的成就。
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
他们所记录的证据,来自最早见证和传递上帝讯息之人。
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
由于我从始至终都参与其中,所以应该可以准确无误地撰写所发生的一切。
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
敬爱的提阿非罗们,我之所以这么做,是为了让你们确认自己所学之道完全值得信赖。
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
希律担任犹太王的那段时间,亚比雅班里有一位名叫撒迦利亚的祭司,他妻子以利沙伯是亚伦的后人。
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
他们的一举一动都遵循上帝正道,严格遵守主所立下的一切诫命规条。
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
但他们没有孩子,因为以利沙伯无法生育,而且二人都年岁已高。。
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
有一天,撒迦利亚按照排班的时间履行作为上帝祭司的职责,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
照惯例抽签后,他被选中进入主的神庙上香。
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
在烧香的过程,众人都在外面祈祷。
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
这时天使向撒迦利亚显化,立于香坛的右侧。
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
撒迦利亚见状颇感惊慌,非常害怕。
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
天使说:“撒迦利亚,别害怕,上帝听到了你的祈求。你妻子以利沙伯将为你生下一子,你将为他起名为约翰。
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
这孩子会为你带来欢喜和快乐,许多人都会来庆祝他的降生。
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
他将成为主面前的尊者,滴酒不沾,未降生之前便有圣灵附体。
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
他将带领众多以色列人,回到主、也就是他们的上帝身边。
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
他将以以利亚的圣灵和力量走在前,劝说父亲们关爱自己的儿女,规劝悖逆之人走正道,让民众准备好迎接主。”
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
撒迦利亚问天使:“我要如何相信这一切?我老了,我妻子也是一把年纪。”
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
天使回答:“我是上帝面前的加百列,奉命向你传话,告诉你这个好消息。
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
但你并不相信我所说的一切,所以你会失语,直到我所言之事成真,你才能开口说话。”
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
众人正在外面等候撒迦利亚,见他迟迟未从神庙出来,很是奇怪。
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
但他出来时却真的失语了,无法讲话,只能打手势。于是众人意识到刚才在神庙中出现了神迹。
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
他完成自己的职责后便回了家。
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
几天后,他妻子以利沙伯果真怀孕,在家中待了五个月。
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
她说:“这一切是主的旨意,他这样待我,便是要让我不再在世人面前感到羞辱。”
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
在怀孕的第六个月,上帝派天使加百列来到加利利的拿撒勒镇,现身在一个名叫玛利亚的少女面前。
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
玛利亚当时已与一位名叫约瑟夫的男人订婚。
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
天使向她问候,然后对她说“你很幸运,主与你同在。”
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
玛利亚对此颇感困惑,不知道这问候到底意味着什么。
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
天使说:“玛利亚,不要怕!因为上帝已对你施以恩典。
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
你将怀孕生子,那婴儿将起名叫耶稣。
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
他将成为一位伟人,被称为至高上帝之子,上帝将把向其赐予祖先大卫的王位,
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
他将永远统治雅各的家园,他的王国将永续存在。” (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
玛利亚问天使:“但这怎能可能?我还是处女。”
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
天使回答:“圣灵将降临于你,至高上帝将笼罩于你。那即将诞下的婴儿生而神圣,将被称为上帝之子。
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
甚至连你的亲戚以利沙伯都怀孕了,人们说那女人无法生育,现在怀胎已有六个月。
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
对于上帝而言,一切皆有可能。”
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
玛利亚说:“我听你的,随时准备服侍上帝,愿你所言的事情发生在我身上。”于是天使便离开了。
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
稍后,玛利亚准备了一下便急忙赶去犹太山地的一座城市,
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
来到撒迦利亚的家。她走进屋向以利沙伯问安。
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
听见玛利亚的问候,以利沙伯腹中的婴儿立刻开始跳动,表达着喜悦。圣灵注入了以利沙伯的体内,
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
于是她高声说:“你是一位如此有福的女人,你腹中的婴儿能由你诞下,也是一种福气!
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
我太荣幸了,我主之母能够造访我的寒舍。
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
听到你问候的那一刻,我腹中的婴儿就欢喜跳跃。
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
你真荣幸,因为你已确信,主将把对你的承诺变为现实!”
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
玛利亚说:“赞美主!
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
上帝救世主让我如此欢喜,
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
因为我作为他的仆人,尽管身世卑微,他却决定垂青于我。今后万代都会认为我是获得赐福之人。
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
全能上帝对我做出伟大之举,他的名字如此神圣。
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
他的怜悯将在尊敬他的世界中传递。
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
他凭借其力量,击败了那些自作聪明之人。
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
他能够让位高权重之人跌落王位,让谦卑之人获得升华,
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
他让饥肠辘辘之人饱餐美食,也让富足之人两手空空。
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
在他的帮助下,他的仆人以色列将永记他的怜悯, (aiōn g165)
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
正如他向我们先父、亚伯拉罕及其后裔所做的承诺。”
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
玛利亚和以利沙伯同住了三个月,然后便返回自己的家。
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
以利沙伯终于诞下一名男婴。
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
邻居和亲戚们得知主向她施以如此善意,便和她一同庆祝。
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
到了第八天,他们前来为孩子行割礼,打算让他随父亲的名字叫撒迦利亚。
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
但以利沙伯说:“不要,他应该叫做约翰。”
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
众人回答:“但你的亲戚中并没有这样的名字。”
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
他们通过手势询问孩子的父亲撒迦利亚,询问他的意见。
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
撒迦利亚示意要写字。令众人诧异的是,他写下的是:“他就叫约翰。”
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
忽然他再次开口说话了,开始赞美上帝。
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
这一切让住在周围的人心生敬畏,这个消息很快就传遍整个犹太山地。
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
众人听闻此事便思量它的含义:“这孩子将会成为怎样的人?”因为很显然,他对上帝而言非常特别。
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
婴儿的父亲撒迦利亚体内充满了圣灵,他预言道:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
“主就是以色列的上帝,他如此伟大,因为他降临到子民之中,为其赋予自由,
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
他向其仆人大卫的家族赐予伟大的救赎,
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
正如他自古以来借由其神圣先知所传达的预言。 (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
他承诺拯救我们摆脱敌人,远离那些憎恨我们的人。
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
他怜悯我们的祖先,记得他的圣约,
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
那是他向我们的祖先亚伯拉罕所发誓言。
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
他让我们摆脱恐惧,从敌人手中拯救我们,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
这让我们可以毕生遵循正道并服侍于他。
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
尽管你现在只是一个婴儿,但却会被称为至高上帝的先知,因你将先于主之前,为他铺好道路,
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
通过宽恕其子民的罪,传播救赎的讯息。
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
蒙上帝对我们的关爱怜悯,天堂的黎明将降临照耀我们,
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
照亮那些活在黑暗中、笼罩在死亡阴影中的人,引导我们走上平安之路。”
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
这个叫做约翰的男孩逐渐长大,精神变得很强大。他一直住在荒野之中,等待在以色列人中公开露面的时机。

< Luka 1 >