< Firistoci 26 >

1 “‘Kada ku yi gumaka, ko ku kafa siffa, ko al’amudi wa kanku, kada kuma ku sa sassaƙaƙƙun duwatsu a ƙasarku don ku rusuna musu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Machet euch keine Götzen und richtet euch keine Schnitzbilder oder Bildsäulen auf, und setzet kein Steingebilde in eurem Lande, um davor anzubeten; denn Ich, Jeho- vah, bin euer Gott.
2 “‘Ku kiyaye Asabbataina, ku kuma ba wa wuri mai tsarkina girma. Ni ne Ubangiji.
Haltet Meine Sabbathe und fürchtet euch vor Meinem Heiligtum. Ich bin Jehovah.
3 “‘In kuka kiyaye farillaina, kuka yi biyayya da umarnaina,
Wenn ihr nach Meinen Satzungen wandelt und Meine Gebote haltet und sie tuet,
4 zan aika da ruwan sama a lokacinsa, ƙasa kuma za tă ba da hatsi, itatuwa kuma za su haihu’ya’yansu.
So werde Ich eure Regen geben zu ihrer Zeit, und die Erde wird geben ihr Gewächs und der Baum des Feldes wird geben seine Frucht.
5 Masussukanku za su ci gaba har lokacin girbin inabi, girbin inabi kuma zai ci gaba har lokacin shuki, za ku kuma ci duk abincin da kuke so cikin salama a ƙasarku.
Und reichen soll euch das Dreschen bis zur Weinlese, und die Weinlese soll reichen bis zur Aussaat, und sollet euer Brot essen zur Sättigung und in Sicherheit in eurem Lande wohnen
6 “‘Zan ba ku salama a ƙasar, za ku kuwa kwanta, kuma babu wani da zai tsorata ku. Zan kori mugayen namun jeji daga ƙasar, takobi kuma ba zai ratsa cikin ƙasarku ba.
Und Frieden werde Ich im Lande geben, und ihr sollt euch niederlegen und niemand mache euch erzittern, und Ich will das böse wilde Tier aus dem Lande aufhören lassen und kein Schwert soll euer Land durchziehen.
7 Za ku kori abokan gābanku, za su kuwa fāɗi a kaifin takobi a gabanku.
Und ihr werdet nachsetzen euren Feinden und sie sollen vor euch fallen durch das Schwert.
8 Mutanenku biyar za su kori mutum ɗari, mutanenku ɗari kuma za su kori mutane dubu goma, abokan gābanku kuma za su fāɗi a kaifin takobi a gabanku.
Fünf von euch sollen hunderten nachsetzen, und hundert von euch sollen zehntausenden nachsetzen; und eure Feinde sollen vor euch fallen durch das Schwert.
9 “‘Zan dube ku da idon rahama, in kuma sa ku riɓaɓɓanya ku kuma ƙaru, zan kiyaye alkawarina da ku.
Und Ich will Mich zu euch wenden und euch fruchtbar machen und euch mehren, und aufrichten Meinen Bund mit euch.
10 Za ku ci gaba da cin girbin bara, har ku fitar da shi don ku sami wurin saboda sabo.
Alt gewordenes Altes sollt ihr essen und das Alte hinausbringen vor dem Neuen.
11 Zan kafa wurin zamana a cikinku, ba zan kuma yi ƙyamarku ba.
Und Meine Wohnung will Ich in eure Mitte setzen, und Meine Seele wird euer nicht überdrüssig werden.
12 Zan yi tafiya a cikinki in kuma zama Allahnku, za ku kuwa zama mutanena.
Und Ich will in eurer Mitte ziehen und ein Gott euch sein, und ihr sollt sein Mein Volk.
13 Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar don kada ku ƙara zama bayi ga Masarawa; na karya sandunan wahalarku, na kuma bar ku ku yi tafiya a sake.
Ich, Jehovah, bin euer Gott, Der euch aus Ägyptenland herausgebracht, daß ihr nicht ihre Knechte wäret, und brach eures Joches Stäbe, und ließ euch aufrecht gehen.
14 “‘Amma in za ku kasa kunne gare ni, ku kuma aikata dukan waɗannan umarnai,
Höret ihr aber nicht auf Mich und tut nicht alle diese Gebote,
15 in kuka kuma ƙi farillaina, kuka yi ƙyamar dokokina, kuka kuma kāsa kiyaye umarnaina, har kuka karya alkawarina,
Und verschmähet Meine Satzungen und eure Seele wird Meiner Rechte überdrüssig, so daß ihr nicht alle Meine Gebote tut, so daß ihr Meinen Bund zunichte macht,
16 to, zan yi muku wannan. Zan kawo muku abin bantsoro, cututtuka da zazzaɓin da zai lalatar da idonku, yă kuma sa ranku a wahala. Za ku shuka iri a banza, domin abokan gābanku ne za su ci.
So will auch Ich euch solches tun: Und Ich werde euch heimsuchen mit Bestürzung, Schwindsucht und Fieberglut, so daß die Augen sich verzehren und eure Seele vergeht. Vergeblich sollt ihr euren Samen säen und eure Feinde sollen ihn essen.
17 Zan yi gāba da ku har abokan gābanku su ci ku a yaƙi, su waɗanda suke ƙinku za su yi mulki a kanku, za ku gudu ba tare da wani yana korinku ba.
Und Ich werde Mein Angesicht wider euch setzen, daß ihr geschlagen werdet vor euren Feinden und eure Hasser euch unterwerfen, und ihr fliehet, da euch niemand nachsetzt.
18 “‘In bayan dukan wannan, ba ku saurare ni ba, zan hukunta ku saboda zunubanku har sau bakwai.
Und höret ihr über diesem noch nicht auf Mich, so werde Ich euch siebenfach mehr ob euren Sünden züchtigen;
19 Zan karya ikonku wanda kuke fariya da shi, in hana ruwan sama, ƙasa kuma tă zama kamar tagulla.
Und will brechen den Stolz eurer Stärke und euern Himmel wie Eisen, und euer Land euch wie Erz machen;
20 Ƙarfinku zai ƙare a banza domin ƙasarku ba za tă ba da hatsi ba, balle itatuwan ƙasar su ba da’ya’ya.
Zu Ende kommen soll eure Kraft vergeblich; und das Land wird sein Gewächs nicht geben und der Baum des Landes nicht geben seine Frucht.
21 “‘In kuka ci gaba da tayar mini, kuka ƙi ku saurare ni, zan ninka wahalolinku sau bakwai, yadda ya dace da zunubanku.
Und wandelt ihr Mir zuwider und wollet nicht auf Mich hören, so füge Ich siebenmal mehr Schläge hinzu nach euren Sünden,
22 Zan aika da mugayen namun jeji a kanku, za su kuwa kashe’ya’yanku, su hallaka shanunku, su rage yawanku, ku zama kaɗan. Wannan zai sa a rasa mutane a kan hanyoyinku.
Und sende wider euch das wilde Tier des Feldes, und es soll euch kinderlos machen und ausrotten euer Vieh, und mache euer weniger, und mache eure Straßen wüste.
23 “‘In duk da waɗannan abubuwa, ba ku yarda da gyaran da nake yi muku ba, kuka ci gaba da yin adawa da ni,
Und lasset ihr auch damit euch noch nicht von Mir züchtigen und wandelt Mir zuwider,
24 zan yi adawa da ku, zan kuma aukar muku saboda zunubanku har sau bakwai.
So gehe auch Ich wider euch und schlage euch, auch Ich, noch siebenfach um eurer Sünden willen.
25 Zan kawo takobi a kanku don in yi ramuwa saboda karya alkawarin da kuka yi. Sa’ad da kuka janye zuwa cikin biranenku, zan aika da annoba a cikinku, za a kuwa ba da ku ga hannun abokan gāba.
Und bringe über euch das Schwert der Rache, das den Bund rächet. Und ihr werdet euch in eure Städte sammeln, Ich aber werde die Pest in eure Mitte senden, und ihr werdet in des Feindes Hand gegeben.
26 Sa’ad da na yanke abincinku, mata goma za su dafa abinci a murhu ɗaya, za su kuma rarraba abincin a ma’auni. Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba.
Wenn Ich euch den Stab des Brotes zerbrechen werde, und zehn Weiber werden euer Brot in einem Ofen backen und euer Brot nach dem Gewicht zurückgeben, und ihr es sollet essen und nicht gesättigt werden.
27 “‘In duk da haka kuka ci gaba da ƙin saurare ni, kuka ci gaba da yin adawa da ni,
Und so ihr trotzdem nicht auf Mich höret und wandelt Mir zuwider:
28 cikin fushina, sai in yi adawa da ku, in kuma hukunta ku saboda zunubanku har sau bakwai.
So gehe Ich im Grimme der Begegnung wider euch, daß Ich, auch Ich, euch züchtige siebenfach ob euren Sünden;
29 Za ku ci naman’ya’yanku maza da na’ya’yanku mata.
Und ihr werdet essen eurer Söhne Fleisch und eurer Töchter Fleisch werdet ihr essen.
30 Zan rurrushe dukan masujadanku, in yanke bagadanku na turare, in yi tarin gawawwakinku a kan gumakanku, zan kuma yi ƙyamarku.
Vernichten werde Ich eure Opferhöhen und ausrotten eure Sonnensäulen und eure Leichen auf eurer Götzen Leichen legen, und Meine Seele euch verwerfen.
31 Zan mai da biranenku kango, in lalace wuraren tsarkinku, ba zan kuma shaƙi ƙanshi hadayunku ba.
Und Ich werde eure Städte öde machen und verwüsten eure Heiligtümer, und nicht den Geruch eurer Ruhe riechen.
32 Zan mai da ƙasarku kango har abokan gābanku da suke zama a wurin su yi mamaki.
Und Ich werde verwüsten das Land, daß eure Feinde, die darin wohnen, sich darob entsetzen werden.
33 Zan watsar da ku cikin al’ummai, in kuma ja takobina in kore ku. Ƙasarku za tă zama kufai, biranenku kuma su zama kango.
Und Ich werde euch zersprengen unter die Völkerschaften und ausziehen ein Schwert hinter euch her, und euer Land soll eine Wüste und eure Städte eine Öde werden.
34 Sa’an nan ƙasar za tă ji daɗin hutun shekarun Asabbacinta, a dukan lokutan da take kango, ku kuwa kuna a ƙasar abokan gābanku, sa’an nan ƙasar za tă huta ta ji daɗin asabbatanta.
Dann läßt sich wohlgefallen das Land seine Sabbathe alle Tage, die es wüste ist und ihr im Land eurer Feinde seid; dann wird das Land feiern und läßt sich wohlgefallen seine Sabbathe.
35 A dukan lokutan da take kango, ƙasar za tă sami hutun da ba tă samu a lokutan asabbatan da kuke zama a cikinta ba.
Alle Tage des Wüsteliegens feiert es dann, wie es nicht gefeiert an euren Sabbathen, da ihr noch darin wohntet.
36 “‘Ga waɗanda za su ragu kuwa, zan cika zukatansu da tsoro a ƙasashen abokan gābansu har motsin ganyen da iska ta hura zai sa su ruga da gudu. Za su yi gudu kamar suna gudu daga takobi ne, za su kuma fāɗi, ko da yake babu wanda yake korinsu.
Und die von euch, so verblieben: Verzagtheit will Ich bringen in ihr Herz, in ihrer Feinde Landen, daß sie jagt das Rauschen eines dahingetriebenen Blattes und sie fliehen, wie man vor dem Schwerte flieht, und fallen, da niemand ihnen nachsetzt.
37 Za su yi karo da juna kamar waɗanda suke tsere wa takobi, ko da yake babu wanda yake korinsu. Ta haka ba za ku iya tsaya a gaban abokan gābanku ba.
Und der Mann wird straucheln über seinen Bruder, wie vor dem Schwerte, wo ihnen niemand nachsetzt und ihr vor euren Feinden nicht bestehen könnt.
38 Za ku mutu a cikin al’ummai, ƙasar abokan gābanku za tă cinye ku.
Unter den Völkerschaften geht ihr zugrunde, und eurer Feinde Land frißt euch auf.
39 Sauranku da suka ragu za su lalace a ƙasashen abokan gābansu saboda zunubansu; da kuma saboda zunuban kakanninsu.
Und die von euch, so verblieben, vergehen durch ihre Missetat in ihrer Feinde Landen, und auch durch ihrer Väter Missetaten vergehen sie mit ihnen.
40 “‘Amma in suka tuba daga zunubansu da zunuban kakanninsu, da cin amanar da suka yi mini, da kuma adawar da suka yi da ni,
Und sie werden bekennen ihre Missetat und die Missetat ihrer Väter damit, daß sie Mir abgefallen und Mir zuwider gewandelt sind.
41 waɗanda suka sa na yi adawa da su har da na aika da su ƙasar abokan gābansu, sa’ad da suka ƙasƙantar da zukatansu marasa kaciya, suka kuma biya hukuncin zunubansu,
Darum werde Ich auch wider sie gehen, und sie in das Land ihrer Feinde bringen, ob nicht dann ihr unbeschnittenes Herz sich niederbeuge und sie dann ihre Missetat abtragen.
42 zan tuna da alkawarina da Yaƙub, da alkawarina da Ishaku, da kuma alkawarina da Ibrahim, zan tuna da ƙasar.
Und Ich werde gedenken an Meinen Bund mit Jakob und auch an Meinen Bund mit Isaak und auch an Meinen Bund mit Abraham werde Ich gedenken, und an das Land gedenken.
43 Gama za su gudu su bar ƙasar, ƙasar kuwa ta ji daɗin asabbatanta yayinda take kango muddin ba su ciki. Za su biya hukuncin zunubansu domin sun ƙi dokokina, suka kuma yi ƙyamar farillaina.
Und das Land wird von ihnen verlassen sein und seine Sabbathe sich gefallen lassen, während es von ihnen wüste gelassen wird, sie selbst aber werden ihre Missetat abtragen, weil und weil sie Meine Rechte verschmäht und ihre Seele Meiner Satzungen überdrüssig geworden ist.
44 Duk da haka, sa’ad da suke a ƙasar abokan gābansu, ba zan ƙi su, ko in yi ƙyamarsu, in hallaka su ƙaƙaf, har in karya alkawarina da su ba. Ni ne Ubangiji Allahnsu.
Und selbst da noch, während sie im Lande ihrer Feinde sind, habe Ich sie nicht verschmäht und ihrer nicht so überdrüssig geworden, daß Ich sie wegtilgte und Meinen Bund mit ihnen zunichte machte; denn Ich, Jehovah, bin ihr Gott.
45 Amma saboda su, zan tuna da alkawarin da na yi da kakanninsu, waɗanda na fitar da su daga Masar a idon al’ummai, don in zama Allahnsu. Ni ne Ubangiji.’”
Und Ich gedenke für sie an den Bund mit den Vorfahren, die Ich vor den Augen der Völkerschaften aus Ägyptenland herausgebracht, um ihnen ein Gott zu sein. Ich, Jehovah.
46 Waɗannan su ne farillai, da dokoki, da kuma ƙa’idodin da Ubangiji ya kafa a Dutsen Sinai, tsakaninsa da Isra’ilawa ta wurin Musa.
Dies sind die Satzungen und die Rechte und Gesetze, die Jehovah zwischen Sich und zwischen den Söhnen Israels auf dem Berge Sinai durch die Hand Moses gegeben hat.

< Firistoci 26 >