< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
I AM the man that hath seen affliction by the rod of his wrath.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
He hath led me and caused me to walk in darkness and not in light.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Surely against me he turneth his hand again and again all the day.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
My flesh and my skin hath he made old; he hath broken my bones.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
He hath builded against me, and compassed me with gall and travail.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
He hath made me to dwell in dark places, as those that have been long dead.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
He hath fenced me about, that I cannot go forth; he hath made my chain heavy.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Yea, when I cry and call for help, he shutteth out my prayer.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
He hath fenced up my ways with hewn stone, he hath made my paths crooked.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
He is unto me as a bear lying in wait, as a lion in secret places.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
He hath turned aside my ways, and pulled me in pieces; he hath made me desolate.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
He hath bent his bow, and set me as a mark for the arrow.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
He hath caused the shafts of his quiver to enter into my reins.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
I am become a derision to all my people; and their song all the day.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
He hath filled me with bitterness, he hath sated me with wormwood.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
He hath also broken my teeth with gravel stones, he hath covered me with ashes.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
And thou hast removed my soul far off from peace; I forgat prosperity.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
And I said, My strength is perished, and mine expectation from the LORD.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Remember mine affliction and my misery, the wormwood and the gall.
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
My soul hath them still in remembrance, and is bowed down within me.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
This I recall to my mind, therefore have I hope.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
[It is of] the LORD’S mercies that we are not consumed, because his compassions fail not.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
They are new every morning; great is thy faithfulness.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
The LORD is my portion, saith my soul; therefore will I hope in him.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
The LORD is good unto them that wait for him, to the soul that seeketh him.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
It is good that a man should hope and quietly wait for the salvation of the LORD.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
It is good for a man that he bear the yoke in his youth.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Let him sit alone and keep silence, because he hath laid it upon him.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Let him put his mouth in the dust; if so be there may he hope.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Let him give his cheek to him that smiteth him; let him be filled full with reproach.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
For the Lord will not cast off for ever.
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
For though he cause grief, yet will he have compassion according to the multitude of his mercies.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
For he doth not afflict willingly, nor grieve the children of men.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
To crush under foot all the prisoners of the earth,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
To turn aside the right of a man before the face of the Most High,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
To subvert a man in his cause, the Lord approveth not.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Who is he that saith, and it cometh to pass, when the Lord commandeth it not?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Out of the mouth of the Most High cometh there not evil and good?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Wherefore doth a living man complain, a man for the punishment of his sins?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Let us search and try our ways, and turn again to the LORD.
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Let us lift up our heart with our hands unto God in the heavens.
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
We have transgressed and have rebelled; thou hast not pardoned.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Thou hast covered with anger and pursued us; thou hast slain, thou hast not pitied.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Thou hast covered thyself with a cloud, that [our] prayer should not pass through.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Thou hast made us [as] the offscouring and refuse in the midst of the peoples.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
all our enemies have opened their mouth wide against us.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Fear and the pit are come upon us, devastation and destruction.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Mine eye runneth down with rivers of water, for the destruction of the daughter of my people.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mine eye poureth down, and ceaseth not, without any intermission,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Till the LORD look down, and behold from heaven.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Mine eye affecteth my soul, because of all the daughters of my city.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
They have chased me sore like a bird, that are mine enemies without cause.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
They have cut off my life in the dungeon, and have cast a stone upon me.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Waters flowed over mine head; I said, I am cut off.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
I called upon thy name, O LORD, out of the lowest dungeon.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Thou heardest my voice; hide not thine ear at my breathing, at my cry.
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Thou drewest near in the day that I called upon thee: thou saidst, Fear not.
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
O Lord, thou hast pleaded the causes of my soul; thou hast redeemed my life.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
O LORD, thou hast seen my wrong; judge thou my cause.
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Thou hast seen all their vengeance and all their devices against me.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Thou hast heard their reproach, O LORD, and all their devices against me;
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
The lips of those that rose up against me, and their imagination against me all the day.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Behold thou their sitting down, and their rising up; I am their song.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Thou wilt render unto them a recompence, O LORD, according to the work of their hands.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Thou wilt give them hardness of heart, thy curse unto them.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Thou wilt pursue them in anger, and destroy them from under the heavens of the LORD.

< Makoki 3 >