< Mahukunta 9 >

1 Abimelek ɗan Yerub-Ba’al ya tafi Shekem wurin’yan’uwan mahaifiyarsa, ya ce musu da kuma dukan dangin mahaifiyarsa,
Gideon’s son Abimelech went to [talk with] his mother’s brothers in Shechem [city]. He said to them and to all his mother’s relatives,
2 “Ku tambayi’yan ƙasar Shekem, ‘Wanne ya fi muku, a sa dukan’ya’yan Yerub-Ba’al saba’in maza su yi mulkinku, ko dai mutum guda kawai yă yi mulkinku?’ Ku tuna, ni jininku ne.”
“Ask all the leaders of your city: ‘Do you [think it would be] good for all 70 of Gideon’s sons to rule over you? Or would it be better to have only one of his sons, [me], to rule over you?’ And do not forget that I am your relative! [MTY]”
3 Sa’ad da’yan’uwan suka mayar wa’yan ƙasar Shekem wannan, sai suka goyi bayan Abimelek, gama sun ce, “Shi ɗan’uwanmu ne.”
So Abimelech’s mother’s brothers spoke to all the leaders of Shechem about what Abimelech had said. They said to each other, “We should allow Abimelech to rule over us, because he is our relative.”
4 Suka ba shi shekel saba’in na azurfa daga haikalin Ba’al-Berit, Abimelek kuwa ya yi amfani da shi ya yi hayar’yan tauri waɗanda suka zama masu binsa.
So the leaders of Shechem took from the temple of [their god] Baal-Berith (almost 2 pounds/0.8 kg.) of silver and gave it to Abimelech. With that silver he paid some worthless troublemakers to help him, and they went with Abimelech wherever he went.
5 Sai ya tafi gidan mahaifinsa a Ofra kuma a dutse guda ya kashe’yan’uwansa,’ya’yan Yerub-Ba’al. Amma Yotam, autan ɗan Yerub-Ba’al ya tsira ta wurin ɓuya.
They went to Ophrah, his father’s town, and murdered 69 of his 70 brothers, the sons of his father Gideon. They killed all those men on one huge rock. But Gideon’s youngest son Jotham hid [from Abimelech and his men], and he escaped.
6 Sa’an nan duka’yan ƙasar Shekem da Bet Millo suka taru kusa da babban itacen wajen ginshiƙi a Shekem don a naɗa Abimelek sarki.
Then all the leaders of Shechem and Beth-Millo gathered under the big sacred tree in Shechem. There they appointed Abimelech to be their leader.
7 Sa’ad da aka gaya wa Yotam wannan, sai ya hau Dutsen Gerizim ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku saurare ni,’yan ƙasar Shekem, don Allah yă saurare ku.
When Jotham heard about that, he climbed up Gerizim Mountain. He stood at the top of the mountain and shouted to the people [down below], “You leaders of Shechem, listen to me, in order that God will listen to you!
8 Wata rana itatuwa suka fita don su naɗa wa kansu sarki. Suka ce wa itacen zaitun, ‘Ka zama sarkinmu.’
One day the trees decided to appoint a king to rule over all of them. So they said to the olive tree, ‘You be our king!’
9 “Amma itacen zaitun ya ce, ‘In bar mai nawa, wanda da shi ake girmama alloli da mutane, don in zo in yi ta fama da itatuwa?’
“But the olive tree said, ‘No! [I will not be your king] Men and gods enjoy the oil from my fruit. I will not [RHQ] stop producing [olives from which we make] that oil, in order to rule over you other trees!’
10 “Biye da wannan, sai itatuwan suka ce wa itacen ɓaure, ‘Zo ka zama sarkinmu.’
“Then the trees said to the fig tree, ‘You come and be our king!’
11 “Amma itacen ɓauren ya ce, ‘In bar kyawawan’ya’yana da zaƙinsu, in zo in yi ta fama da itatuwa?’
“But the fig tree replied, ‘No! I do not want to [RHQ] stop producing my good sweet fruit, and rule over you other trees!’
12 “Sa’an nan itatuwan suka ce wa kuringar inabi, ‘Ki zo ki zama sarkinmu.’
“Then the trees said to the grapevine, ‘Come and be our king!’
13 “Amma kuringar ta ce, ‘In bar ruwan inabina, wanda yake faranta zuciyar alloli da mutane, in zo in yi fama da itatuwa?’
“But the grapevine replied, ‘No! [I will not be your king] The new wine [that is made from my grapes] causes people and gods [who drink it] to become very happy. I do not want to stop producing grapes and rule over you other trees!’ [RHQ]
14 “A ƙarshe sai dukan itatuwa suka ce wa itacen ƙaya, ‘Ka zo ka zama sarkinmu.’
“Then all the trees said to the thornbush, ‘Come and be our king!’
15 “Itacen ƙaya ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske ne kuke so ku naɗa ni sarkinku, ku zo ku sha inuwana; in ba haka ba, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al’ul na Lebanon!’
“The thornbush replied, ‘If you truly want to appoint me to be your king, come into the shade of my [tiny branches]. But if you do not want to do that, I hope/desire that fire will come out from me and burn up all the huge cedar trees in Lebanon [country]!’”
16 “To, da a ce kun yi abin bangirma da aniya mai kyau sa’ad da kuka naɗa Abimelek sarki, da kun nuna wa Yerub-Ba’al da iyalinsa ladabi, da kuma kun yi masa abin da ya cancanci shi,
“[After] Jotham [finished telling them this parable, he] said, “So now [I ask you], were you being completely honest and sincere when you appointed Abimelech to be your king [RHQ]? And have you treated Gideon and his family [RHQ] fairly? Have you rewarded Gideon by honoring him as he deserved [because of all the good things he did for you]? No!
17 a yi tunani cewa mahaifina ya yi yaƙi saboda ku, ya yi kasai da ransa don yă cece ku daga hannun Midiyawa
“[Do not forget that] my father fought a battle for you, and he was willing to die for you [if that had been necessary], to save you from the Midian people-group.
18 (amma ga shi yau kun tayar wa iyalin mahaifina, kuka kashe’ya’yansa saba’in a dutse guda, kuka kuma naɗa Abimelek, ɗan baiwa, sarki a kan’yan ƙasar Shekem domin shi ɗan’uwanku ne)
But now you have rebelled against my father’s family, and you have killed 69 of his sons on one huge rock. And you have appointed Abimelech—who is the son of my father’s slave girl, [not the son of his wife]—to be the king who will rule you people of Shechem. You have done that only because he is one of your relatives!
19 in har kun aikata wannan cikin bangirma da kuma aminci wajen Yerub-Ba’al da iyalinsa a yau, bari Abimelek yă zama farin cikinku, ku kuma nasa!
So, if today you have truly acted fairly and sincerely toward Gideon and his family, I hope/desire that he will cause you to be happy and that you will cause him to be happy.
20 Amma in ba haka ba, bari wuta ta fito daga Abimelek ya cinye ku,’yan ƙasar Shekem da Bet Millo, bari wuta kuma daga wurinku’yan ƙasar Shekem da Bet Millo ta cinye Abimelek!”
But if what you did was not right, I wish/desire that Abimelech will burn up all of you leaders of Shechem and Beth-Millo with fire! And I also hope/desire that the leaders of Shechem and Beth-Millo will cause fire to burn up Abimelech!”
21 Sa’an nan Yotam ya gudu, ya tsere zuwa Beyer ya zauna a can gama yana tsoron ɗan’uwansa Abimelek.
[After] Jotham [finished saying that, he] escaped from them and ran away to Beer [town]. He stayed there because he was afraid that his brother Abimelech [would try to kill him].
22 Bayan Abimelek ya yi shekara uku yana mulki a Isra’ila,
Abimelech [became the leader of all the people of Israel. He] ruled them for three years.
23 sai Allah ya aiko da mugun ruhu tsakanin Abimelek da’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka ci amanar Abimelek.
Then God sent an evil spirit [to cause trouble] between Abimelech and the leaders of Shechem, with the result that the leaders of Shechem rebelled against Abimelech.
24 Allah ya yi haka saboda kisan’ya’ya saba’in na Yerub-Ba’al, don a ɗauki fansar jininsu a kan Abimelek ɗan’uwansu da kuma’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka taimake shi kisan’yan’uwansa.
The leaders of Shechem had previously helped Abimelech to kill 69 of Gideon’s sons, who were his brothers. So now God sent the evil spirit to punish all of them.
25 Cikin hamayya da shi waɗannan’yan ƙasar Shekem suka sa mutane a kan tuddai don su yi kwanton ɓauna a kan su yi fashi ga duk wanda ya wuce a can, wannan fa ya kai kunnen Abimelek.
The leaders of Shechem (set an ambush/sent men to hide) on the hilltops to ambush Abimelech. Those men robbed everyone who passed by. But someone told Abimelech about it, [so he did not go near them].
26 To, Ga’al ɗan Ebed ya tafi tare da’yan’uwansa zuwa Shekem,’yan ƙasarta kuwa suka dogara da shi.
There was a man named Gaal, the son of Ebed, who moved into Shechem [city], along with his brothers. Soon the leaders of Shechem started to trust him.
27 Bayan sun tafi gonaki suka tattara inabi suka matse su, sai suka yi biki a haikalin allahnsu. Yayinda suke ci da sha, sai suka la’anci Abimelek.
They went out [of the city] to their vineyards and picked some grapes. They pressed the grapes [to make juice, and then they made wine]. Then they had a feast in the temple of their god, and they ate [a lot of food] and drank [a lot of wine]. Then they cursed Abimelech.
28 Sa’an nan Ga’al ɗan Ebed ya ce, “Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem, da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub-Ba’al ba ne, kuma ba Zebul ne mataimakinsa ba? Ku bauta wa mutanen Hamor, mahaifin Shekem! Me ya sa za mu bauta wa Abimelek?
Gaal said, “(Why should [we allow] Abimelech to rule over us?/We should not allow Abimelech to rule over us!) [RHQ] He is only one of Gideon’s sons [so he really does not belong to us] [RHQ]! And he appointed Zebul, the governor of our city, to be his deputy! We should (serve/be loyal to) [one of the descendants of] Hamor, [the founder of our city], and let him be our leader, not Abimelech [RHQ]!
29 Da a ce waɗannan mutane suna a ƙarƙashina mana! Da zan hamɓarar da shi. In ce wa Abimelek, ‘Ka tara dukan mayaƙanka!’”
If you would appoint me to be your leader, I would get rid of Abimelech. I would say to him, ‘Get your army ready, [and then come to fight us]!’”
30 Sa’ad da Zebul gwamnar birnin ya ji abin da Ga’al ɗan Ebed ya ce, sai ya fusata.
When someone told Zebul what Gaal said, he was very angry.
31 Asirce sai ya aiki manzanni wajen Abimelek, yana cewa, “Ga’al ɗan Ebed da’yan’uwansa sun zo Shekem suna kuma zuga birnin sun tayar maka.
He secretly sent some messengers to Abimelech. They told him, “Gaal and his brothers have come here to Shechem, and they are causing [the people of] the city to rebel against you.
32 To, in dare ya yi, sai ka zo da mutanenka ku yi kwanto a filaye.
You and your men should get up during the night and go and hide in the fields outside the city.
33 Kashegari da safe, sai ku tashi ku fāɗa wa birnin. Sa’ad da Ga’al da mutanensa suka faɗa maka, sai ka yi abin da ka iya yi da su.”
As soon as the sun rises in the morning, get up and attack the city. When Gaal and his men come out to fight against you, you can do to them whatever you want to.”
34 Saboda haka Abimelek da dukan mutanensa suka tashi da dare suka ɓuya kusa da Shekem a ƙungiyoyi huɗu.
So Abimelech and all the men who were with him got up during the night. They [divided into] four groups, [and] hid [in the fields] near Shechem.
35 To, Ga’al ɗan Ebed ya riga ya fita waje yana tsaye a ƙofar birni daidai Abimelek da mayaƙansa suka fito daga inda suka ɓuya.
[The next morning], Gaal went out and stood at the entrance to the city gate. While he was standing there, Abimelech and his soldiers came out of their hiding places [and started walking toward the city].
36 Sa’ad da Ga’al ya gan su, sai ya ce wa Zebul, “Duba, ga mutane suna gangarowa daga kan duwatsu!” Zebul ya ce, “Kana ɗaukan inuwan duwatsu kana ce mutane.”
When Gaal saw the soldiers, he said to Zebul, “Look! There are people coming down from the hills!” But Zebul said, “You are seeing only the shadows [of trees] on the hills. They [are not people; they] only resemble people.”
37 Amma Ga’al ya sāke magana ya ce, “Duba, mutane suna gangarowa daga tsakiyar filaye, kuma wata ƙungiya tana zuwa daga wajen itacen masu duba.”
But Gaal [looked] again [and] said, “Look! There are people coming down from the top of the sacred mountain! There is a group of them coming down from where the tree is where people talk with the spirits of dead people!”
38 Sa’an nan Zebul ya ce masa, “Ina bakin da ka yi ɗin, kai da ka ce, ‘Wane ne Abimelek da za mu bauta masa.’ Ba mutanen ne ka yi musu ba’a ba? Fita, ka yaƙe su mana!”
Zebul said to Gaal, “Now (what good is your bragging?/your bragging is worthless!) [MTY, RHQ] You said, ‘(Why should we serve Abimelech/We should not allow Abimelech to rule over us)?’ You made fun of these men. So now go out and fight them!”
39 Saboda haka Ga’al ya fito da’yan ƙasar Shekem suka yaƙi Abimelek.
So Gaal led the men of Shechem outside [the city] to fight Abimelech [and his men].
40 Abimelek ya kore shi, mutane da yawa suka ji ciwo a yaƙin, har zuwa ƙofar birnin.
Abimelech and his men pursued them, and they killed many of Gaal’s men before they could return [safely] inside the city gate.
41 Abimelek ya zauna a Aruma, Zebul kuwa ya kori Ga’al da’yan’uwansa daga Shekem.
Abimelech then stayed at Arumah, [about five miles away from Shechem], and Zebul’s men forced Gaal and his brothers to leave Shechem.
42 Kashegari mutanen Shekem suka tafi gonaki, aka kuwa gaya wa Abimelek.
The next day, the people of Shechem [got ready to leave the city and work] in their fields. When someone told Abimelech about that,
43 Saboda haka ya ɗauki mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, sa’an nan ya yi kwanto a gonakin. Sa’ad da ya ga mutanen suna fitowa daga birni, sai ya yi wuf ya fāɗa musu.
he divided his men into three groups, and told them to hide in the fields. So they did that. And when they saw the people coming out of the city, they jumped up and attacked them.
44 Abimelek da ƙungiyoyin da suke tare da shi suka yi maza suka yi tsaya a ƙofar birnin. Sa’an nan ƙungiyoyi biyu suka ruga suka fāɗa wa waɗanda suke a gonaki suka karkashe su.
Abimelech and the men who were with him ran to the city gate. The other two groups ran out to the people in the fields and attacked them.
45 Dukan yinin, Abimelek ya matsa yaƙi da birnin sai da ya cinye ta ya kuma kashe mutanenta. Sa’an nan ya hallaka birnin ya barbaza gishiri a kanta.
Abimelech and his men fought all day. They captured the city and killed all the people. They tore down all the buildings, and then they threw salt over the ruins [in order that nothing would grow there again].
46 Da jin haka, sai’yan ƙasa a hasumiyar Shekem suka shiga wurin mafaka a hankalin El-Berit.
When the leaders who lived in the tower/fortress outside of Shechem heard what had happened, they ran and hid inside the [fortress, which was also a] temple of [their god] El-Berith.
47 Da Abimelek ya ji dukan mutanen hasumiyar Shekem sun taru a can,
But someone told Abimelech that all the leaders had gathered there.
48 sai Abimelek da dukan mutanensa suka haura zuwa Dutsen Zalmon. Sai ya ɗauki gatari ya sassare waɗansu rassa, waɗanda ya sa a kafaɗunsa. Ya umarci mutanen da suke tare da shi ya ce, “Sauri, ku yi abin da kuka ga na yi!”
So he and all the men who were with him went up Zalmon Mountain [which is near Shechem]. Abimelech cut some branches of trees with an axe, and put them on his shoulders. Then he said to all the men who were with him, “Quickly, do what I have just done!”
49 Saboda haka mutanen suka sassare rassan itatuwa suka bi Abimelek. Suka tattara su a jikin mafakar suka kuma cinna mata wuta a kan mutanen da suke a ciki. Ta haka dukan mutanen da suke cikin hasumiyar Shekem, wajen maza da mata dubu ɗaya suka mutu.
So his men all cut branches [then carried them down the mountain], following Abimelech. They went to the fortress and piled the branches against its walls. Then they kindled a fire, and the fire burned down the fortress and killed all the people who were inside. So all the people who were inside the fortress—about 1,000 men and women—died.
50 Biye da wannan Abimelek ya tafi Tebez, ya kewaye ta ya kuma cinye ta da yaƙi.
Then Abimelech and his men went to Thebes [city]. They surrounded it and captured it.
51 A cikin birnin, akwai wata hasumiya mai ƙarfi, inda dukan maza da mata, dukan mutanen birnin, suka ɓuya. Suka kulle kansu, suka kuma hau rufin hasumiyar.
But there was a strong tower inside the city. So all the men, women, and leaders of the city ran to the tower. When they were all inside, they locked the door. Then they climbed up to the roof of the tower.
52 Abimelek ya je wajen hasumiya ya kuma auka mata. Amma da ya yi kusa da ƙofar hasumiyar don yă cinna mata wuta,
Abimelech and his men came to the tower and tried to get in the door, [but they could not]. Then Abimelech prepared to light a fire to burn down the door.
53 sai wata mata ta saki ɗan dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa ƙoƙon kansa.
But when Abimelech came near the doorway, a woman [who was on the roof] dropped a big grinding stone on his head, and crushed his skull.
54 Da sauri ya kira mai riƙon masa makami ya ce, “Zaro takobinka ka kashe ni, don kada a ce ‘Mace ce ta kashe shi.’” Saboda haka bawansa ya soke shi, ya mutu.
Abimelech quickly called to the young man who carried Abimelech’s weapons, and said, “Pull out your sword and kill me with it! I do not want people to say ‘It was a woman who killed Abimelech.’” So the young man thrust his sword into Abimelech, and Abimelech died.
55 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga Abimelek ya mutu, sai suka tafi gida.
When the Israeli soldiers saw that Abimelech was dead, they all returned to their homes.
56 Ta haka Allah ya sāka muguntar da Abimelek da ya yi wa mahaifinsa ta wurin kisan’yan’uwansa saba’in.
In that way God punished Abimelech for the evil things that he had done to his father and especially for killing all 69 of his brothers.
57 Allah kuma ya sa muguntar mutanen Shekem suka koma kansu. La’anar Yotam ɗan Yerub-Ba’al kuma ta kama su.
God also punished the men of Shechem for the evil things that they had done. And when those things happened, it fulfilled what Gideon’s son Jotham said when he cursed [Abimelech and the leaders of Shechem].

< Mahukunta 9 >