< Mahukunta 7 >

1 Kashegari da sassafe, Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) da dukan mutanensa suka kafa sansani a maɓulɓulan Harod. Sansanin Midiyawa kuma yana arewa da su a kwari kusa da tudu na More.
Then Jerub Baal (that is, Gideon) rose up early, and all the people who were with him, and they encamped beside the spring of Harod. The camp of Midian was to their north in the valley near the hill of Moreh.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Mutanen da kake da su sun yi mini yawa da zan ba da Midiyawa a hannunsu. Don kada Isra’ila tă yi mini fahariya cewa ƙarfinta ne ya cece su,
Yahweh said to Gideon, “There are too many soldiers for me to give you victory over the Midianites, so that Israel may not boast over me, saying, 'Our own power has saved us.'
3 ka yi shela ga mutane yanzu cewa, ‘Duk wanda ya yi rawan jiki don tsoro, sai yă juya yă bar Dutsen Gileyad.’” Saboda haka mutum dubu ashirin da biyu suka koma, sai mutum dubu goma suka rage.
Now therefore, proclaim in the ears of the people and say, 'Whoever is afraid, whoever trembles, let him return and depart from Mount Gilead.'” So twenty-two thousand people went away, and ten thousand remained.
4 Amma Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai cikin ruwa, in kuma tankaɗe maka su a can. In na ce, ‘Wannan zai tafi da kai,’ to, zai tafi; amma in na ce, ‘Wannan ba zai tafi da kai ba,’ to, ba zai tafi ba.”
Yahweh said to Gideon, “The people are still too many. Take them down to the water, and I will make their number smaller for you there. If I say to you, 'This one will go with you,' he will go with you; but if I say, 'This one will not go with you,' he will not go.”
5 Saboda haka Gideyon ya kai mutanen cikin ruwa. A can Ubangiji ya ce masa, “Ka ware waɗanda suka tanɗi ruwa kamar kare daga waɗanda suka durƙusa suka sha ruwan.”
So Gideon brought the people down to the water, and Yahweh said to him, “Separate everyone who laps up the water, as a dog laps, from those who kneel down to drink.”
6 Mutum ɗari uku sun tanɗi ruwa, dukan sauran kuwa suka durƙusa suka sha ruwan.
Three hundred men lapped. The rest of the men kneeled down to drink water.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa, zan cece ka in kuma ba da Midiyawa a hannuwanku. Ka bar sauran mutane su tafi kowa zuwa wurinsa.”
Yahweh said to Gideon, “With the three hundred men who lapped, I will rescue you and give you victory over the Midianites. Let every other man go back to his own place.”
8 Saboda haka Gideyon ya mai da sauran Isra’ilawa zuwa tentinsu amma ya riƙe mutum ɗari uku waɗanda suka karɓi guzuri da ƙahonin sauran. To, sansanin Midiyawa yana ƙasa da su a kwarin.
So those who were chosen took their supplies and their trumpets. Gideon sent away all the men of Israel, every man to his tent, but he kept the three hundred men. Now the Midian camp was down below him in the valley.
9 A daren nan Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Tashi ka tafi sansaninsu domin zan ba da su a hannuwanka.
That same night Yahweh said to him, “Get up! Attack the camp, for I am going to give you victory over it.
10 In kana tsoron fāɗa musu, sai ka tafi da bawanka Fura
But if you are afraid to go down, go down to the camp with Purah your servant,
11 ka kuma saurari abin da suke faɗi. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali ka auka musu.” Saboda haka sai ya tafi tare da Fura bawansa zuwa sansanin.
and listen to what they are saying, and your courage will be strengthened to attack the camp.” So Gideon went with Purah his servant, down to the guard posts of the camp.
12 Midiyawa, Amalekawa da dukan sauran mutane gabashi suka yi sansani a kwari, kamar fāra. Raƙumansu kuma kamar yashi a bakin teku don sun wuce ƙirge.
The Midianites, the Amalekites, and all the people of the east settled along in the valley, as thick as a cloud of locusts. Their camels were more than could be counted; they were more in number than the grains of the sand on the seashore.
13 Gideyon ya iso daidai wani yana faɗa wa wani aboki mafarkinsa, yana cewa, “Na yi mafarki, na ga dunƙule burodin sha’ir ya fāɗo a tsakiyar sansanin Midiyawa. Ya bugi tentin da ƙarfin da ya sa tenti ta kife a ƙasa.”
When Gideon arrived there, a man was telling a dream to his companion. The man said, “Look! I had a dream, and I saw a round loaf of barley bread tumbling into the camp of Midian. It came to the tent, and hit it so hard that it fell down and turned it upside down, so that it lay flat.”
14 Abokinsa ya ce, “Ai wannan ba wani abu ba ne fiye da takobin Gideyon ɗan Yowash, mutumin Isra’ila. Allah ya ba da Midiyawa da dukan sansani a hannuwansa.”
The other man said, “This is nothing other than the sword of Gideon (the son of Joash), the Israelite. God has given him victory over Midian and all their army.”
15 Da Gideyon ya ji mafarkin da fassararsa, sai ya yi wa Allah sujada. Ya koma sansanin Isra’ila ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku tashi! Ubangiji ya ba da sansanin Midiyawa a hannuwanku.”
When Gideon heard the retelling of the dream and its interpretation, he bowed down in worship. He went back to the camp of Israel and said, “Get up! Yahweh has given you victory over the Midian army.”
16 Ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho da tulu da acibalbal a ciki.
He divided the three hundred men into three groups, and he gave them all trumpets and empty jars, with torches inside each jar.
17 Ya ce musu, “Ku dube ni, ku bi abin da na yi. Sa’ad da na kai sansanin, ku yi daidai abin da na yi.
He said to them, “Look at me and do what I do. Watch! When I come to the edge of the camp, you must do what I do.
18 Sa’ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoninmu, to, ko’ina a kewayen sansanin sai ku busa naku ku kuma yi ihu, ku ce, ‘Don Ubangiji da kuma domin Gideyon.’”
When I blow the trumpet, I and all who are with me, then blow your trumpets also on every side of the entire camp and shout, 'For Yahweh and for Gideon!'”
19 Gideyon da mutum ɗari da suke tare da shi suka kai sansanin da tsakar dare bayan an sauya matsara. Suka busa ƙahoninsu, suka farfashe tulunansu da suke hannuwansu.
So Gideon and the hundred men who were with him came to the edge of the camp, right at the beginning of the middle watch. Just as the Midianites were changing guard, they blew the trumpets and broke the jars that were in their hands.
20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka ɗauki acibalbal a hannuwansu na hagu da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama, sai suka yi ihu, “Takobi don Ubangiji da kuma don Gideyon!”
The three companies blew the trumpets and broke the jars. They held the torches in their left hands and the trumpets in their right hands to blow them. They shouted out, “The sword of Yahweh and of Gideon.”
21 Yayinda kowannensu ya tsaya a inda yake kewaye da sansanin, dukan Midiyawa suka fito da gudu, suna kuka yayinda suke gudu.
Every man stood in his place around the camp and all the Midianite army ran. They shouted and ran away.
22 Sa’ad da aka busa ƙahonin nan ɗari uku sai Ubangiji ya sa Midiyawa suka yi ta saran juna. Mayaƙan suka gudu zuwa Bet-Shitta wajen Zerera har zuwa yankin Abel-Mehola kusa da Tabbat.
When they blew the three hundred trumpets, Yahweh set every Midianite man's sword against his comrades and against all their army. The army fled as far as Beth Shittah toward Zererah, as far as the border of Abel Meholah, near Tabbath.
23 Aka kira dukan Isra’ilawa daga Naftali, Asher da dukan Manasse, suka kuwa fatattaki Midiyawa.
The men of Israel from Naphtali, Asher, and all Manasseh were called out, and they went after Midian.
24 Gideyon ya aiki manzanni zuwa dukan ƙasar tudu ta Efraim cewa, “Ku gangaro ku yaƙi Midiyawa ku ƙwace ruwan Urdun gaba da su har zuwa Bet-Bara.” Saboda haka aka kira dukan mutanen Efraim suka ƙwace ruwan Urdun har zuwa Bet-Bara.
Gideon sent messengers throughout all the hill country of Ephraim, saying, “Go down against Midian and take control of the Jordan River, as far as Beth Barah, to stop them.” So all the men of Ephraim gathered together and took control of the waters, as far as Beth Barah and the Jordan River.
25 Suka kuma kama shugabannin biyu na Midiyawa, Oreb da Zeyib suka kashe Oreb a dutsen Oreb, Zeyib kuma a wurin matsin ruwa inabin Zeyib. Suka fatattaki Midiyawa suka kawo kawunan Oreb da Zeba wurin Gideyon, wanda yake kusa da Urdun.
They captured the two princes of Midian, Oreb and Zeeb. They killed Oreb at the rock of Oreb, and they killed Zeeb at the winepress of Zeeb. They went after the Midianites, and they brought the heads of Oreb and Zeeb to Gideon, who was on the other side of the Jordan.

< Mahukunta 7 >