< Mahukunta 19 >

1 A kwanakin nan Isra’ila ba su da sarki. To, wani Balawe wanda yake zama a wani lungu na ƙasar tudu ta Efraim ya ɗauko wa kansa ƙwarƙwara daga Betlehem cikin Yahuda.
It happened in those days, when there was no king in Israel, that there was a certain Levite sojourning on the farther side of the hill country of Ephraim, who took for himself a secondary wife from Bethlehem Judah.
2 Amma ba tă yi aminci ba. Ta bar shi ta komo gidan mahaifiyarta a Betlehem, a Yahuda. Bayan ta zauna a can wajen wata huɗu,
His secondary wife was angry with him and went away from him to her father's house in Bethlehem of Judah, and was there about four months.
3 sai mijinta ya je wajenta biko don yă rarashe ta komo. Ya tafi tare bawansa da kuma jakuna biyu. Sai ta shigar da shi gidan mahaifinta, sa’ad da mahaifinta ya gan shi, ya marabce shi da murna.
Her husband arose, and went after her, to speak kindly to her, to bring her again, having his servant with him, and a couple of donkeys. And she brought him into her father's house; and when the father of the young woman saw him, he rejoiced to meet him.
4 Surukinsa, mahaifin yarinyar, ya sha kansa, yă dakata; saboda haka ya dakata tare da shi har kwana uku, yana ci yana sha, yana kuma kwanciya a can.
His father-in-law, the young woman's father, welcomed him; and he stayed with him three days. So they ate and drank and stayed there.
5 A rana ta huɗu suka tashi da sassafe ya kuma yi shiri yă tafi, amma mahaifinta yarinyar ya ce wa surukinsa, “Ka ɗan ci wani abu don ka sami ƙarfi; sa’an nan ka tafi.”
It happened on the fourth day, that they arose early in the morning, and he rose up to depart: and the young woman's father said to his son-in-law, "Refresh yourself with a piece of bread, and after that you may go."
6 Saboda haka suka zauna su biyu suka ci suka sha tare. Bayan haka sai mahaifin yarinyar ya ce, “Don Allah ka kwana ka ji wa kanka daɗi.”
So they sat down, ate, and drank, both of them together. Then the young woman's father said to the man, "Please agree to stay the night, and enjoy yourself."
7 Sa’ad da mutumin ya tashi zai tafi, sai surukinsa ya roƙe shi, saboda haka ya kwana a wannan dare.
The man rose up to depart; but his father-in-law urged him, and he stayed there again.
8 Da sassafen kashegari rana ta biyar, ya tashi zai tafi, sai mahaifin yarinyar ya ce, “Ka ɗan zauna ka shaƙata sai rana ta yi sanyi mana!” Saboda haka su biyu suka zauna suka ci abinci tare.
He arose early in the morning on the fifth day to depart; and the young woman's father said, "Please refresh yourself and stay until the day declines." And the two of them ate and drank.
9 Sa’ad da mutumin da ƙwarƙwaransa da bawansa, suka tashi don su tafi, surukinsa, mahaifin yarinyar ya ce, “Duba, rana ta kusan fāɗuwa, yamma ta riga ta yi, ka kwana a nan. Ka sāke kwana ka ji wa ranka daɗi. Kashegari da sassafe za ka iya tashi ka kama hanyarka zuwa gida.”
When the man rose up with his secondary wife and his servant to leave, his father-in-law, the young woman's father, said to him, "Look, now the day draws toward evening, please stay the night. Look, the day grows to an end, stay here, and enjoy yourself; and tomorrow you can get up early for your journey so that you may go home."
10 Amma bai so ya sāke kwana a can ba, mutumin ya tashi ya tafi ya bi ta Yebus (wato, Urushalima), tare da jakunansa biyu da aka yi musu shimfiɗa da kuma ƙwarƙwaransa.
But the man wouldn't stay that night, but he rose up and departed, and went toward Jebus (that is, Jerusalem). And there were with him a couple of saddled donkeys, and his secondary wife and his servant were with him.
11 Sa’ad da suka yi kusa da Yebus dare kuma ya riga ya yi, bawan ya ce wa maigidansa, “Mu dakata a birnin nan na Yebusiyawa mu kwana.”
When they were by Jebus, the day was almost gone, and the servant said to his master, "Please come and let us stop at this city of the Jebusites, and spend the night in it."
12 Maigidansa ya ce, “A’a. Ba za mu shiga birnin baƙi waɗanda mutanensu ba Isra’ilawa ba. Za mu ci gaba zuwa Gibeya.”
His master said to him, "We won't go into the city of a foreigner that is not of the children of Israel, but we will pass over to Gibeah."
13 Ya kuma ce, “Zo, mu yi ƙoƙari mu kai Gibeya ko Rama mu kwana a ɗaya cikinsu.”
He said to his servant, "Come and let us try to reach one of those places and we will spend the night in Gibeah or Ramah."
14 Saboda haka suka ci gaba, rana tana fāɗuwa sa’ad da suka yi kusa da Gibeya a Benyamin.
So they passed on and went their way; and the sun set on them near Gibeah, which belongs to Benjamin.
15 A can suka dakata don su kwana, suka tafi suka zauna a dandali birnin, amma wani ya shigar da su gidansa da daren.
They turned that way to go in to spend the night in Gibeah. And he went in and they sat down in the street of the city; for there was no one who would take them into their house to spend the night.
16 A wannan yamma sai ga wani tsoho daga ƙasar tudu ta Efraim, wanda yake zama a Gibeya (mutane wurin kuwa mutanen Benyamin ne), ya shigo daga wurin aiki a gonaki.
Look, there came an old man from his work out in the field at evening. Now the man was of the hill country of Ephraim, and he was residing in Gibeah; but the men of the place were Benjamites.
17 Sa’ad da ya duba ya ga matafiyin a dandalin birnin, sai tsohon ya yi tambaya ya ce, “Ina za ku? Ina kuka fito?”
He lifted up his eyes, and saw the traveler in the street of the city. And the old man said, "Where are you going, and where did you come from?"
18 Balawen ya ce, “Muna fito daga Betlehem a Yahuda za mu wani lungu a ƙasar tudu ta Efraim inda nake da zama. Na tafi Betlehem a Yahuda, ga shi kuwa yanzu za ni gidan Ubangiji. Ba wanda ya shigar da ni gidansa.
He said to him, "We are passing from Bethlehem in Judah to the farther side of the hill country of Ephraim. I am from there, and I went to Bethlehem in Judah. And I am going to my home, and there is no one who will take me into his home.
19 Muna da ƙara da abinci don jakunanmu, muna kuma da burodi da ruwan inabi dominmu da bayinka, ni, baiwarka da kuma saurayin nan tare da mu. Ba ma bukatar kome.”
Yet there is both straw and feed for our donkeys, and there is bread and wine also for me, and for your female servant, and for the young man who is with your servants. There is no lack of anything."
20 Tsohon ya ce, “Na marabce ku a gidana. Bari ni ba ku duk abin da kuke bukata. Kada ku dai kwana a dandali.”
And the old man said, "Peace be to you. I will take care of all your needs; however, do not spend the night in the square."
21 Saboda haka sai kai shi zuwa gidansa ya ciyar da jakunansa. Bayan sun wanke ƙafafunsu, sai aka ba su abinci da abin sha.
So he brought him into his house, and fed the donkeys. And they washed their feet, and ate and drank.
22 Yayinda suke jin wa kansu daɗi, sai waɗansu’yan iska daga birnin suka kewaye gidan. Suna bubbuga ƙofar, suna kira tsohon da yake da gidan suna cewa, “Ka fito mana da mutumin nan a gidanka domin mu yi jima’i da shi.”
As they were enjoying themselves, look, the men of the city, some wicked men of the city surrounded the house, beating at the door. And they spoke to the master of the house, the old man, saying, "Bring out the man who came into your house, that we may have sex with him."
23 Maigidan ya fita waje ya ce musu, “A’a, abokaina, kada ku yi abin kunyan nan. Da yake mutumin nan baƙona ne, kada ku yi rashin kunyan nan.
The man, the master of the house, went out to them, and said to them, "No, my brothers, please do not act so wickedly; since this man has come into my house. Do not do this disgraceful thing.
24 Duba, ga’yata da ba tă taɓa sanin namiji ba da kuma ƙwarƙwaransa. Zan fito muku da su a waje yanzu, za ku kuwa iya yin ko mene ne da kuke so da su. Amma wannan mutum, kada ku yi abin kunya.”
Look, here is my virgin daughter and his secondary wife. I will bring them out now. Ravish them and do with them what seems good to you; but do not do any such a disgraceful thing to this man."
25 Amma mutanen ba su saurare shi ba. Saboda haka mutumin ya ba da ƙwarƙwaransa, suka yi mata fyaɗe suka yi lalata da ita dukan dare, gari yana wayewa sai suka bar ta.
But the men wouldn't listen to him: so the man laid hold of his secondary wife, and brought her out to them. And they raped her and abused her all night until the morning, and when the day began to dawn they let her go.
26 Da safe matar ta koma gidan da maigidanta yake, ta fāɗi a ƙofa ta kwanta a can har rana ta yi.
Then at daybreak the woman arrived and fell down at the door of the man's house where her lord was, until daylight.
27 Sa’ad da maigidanta ya tashi da safe ya buɗe ƙofar gidan don yă fita ya ci gaba da tafiyarsa, sai ga ƙwarƙwararsa, ta fāɗi a bakin ƙofar gidan da hannuwanta a madogarar ƙofar.
Her lord rose up in the morning, and opened the doors of the house, and went out to go his way; and look, the woman his secondary wife was fallen down at the door of the house, with her hands on the threshold.
28 Ya ce mata, “Tashi; mu tafi.” Amma ba amsa. Sai ya sa ta a kan jakinsa ya kama hanyar gida.
And he said to her, "Get up, and let us go." But there was no answer, for she was dead. So he placed her on the donkey, and the man rose up and went to his home.
29 Da ya kai gida, sai ya ɗauki wuƙa ya yayyanka ƙwarƙwaransa gunduwa-gunduwa, kashi goma sha biyu ya aika da su a ko’ina a Isra’ila.
When he had come into his house, he took a knife, and took hold of his secondary wife and divided her, limb by limb, into twelve pieces, and sent her throughout all the territory of Israel.
30 Duk wanda ya gani, sai ya ce, “Ba a taɓa gani ko yin irin wannan abu ba, tun lokacin da Isra’ilawa suka fito daga Masar. Ku yi tunani wannan! Ku kuma yi la’akari! Ku gaya mana abin da za mu yi!”
And it was so, that all who saw it said, "Nothing like this has been done or seen since the day that the children of Israel came up out of the land of Egypt until this day." And he commanded the men whom he sent, saying, "This is what you will say to all the men of Israel, 'Has anything like this happened since the day that the children of Israel came up out of the land of Egypt until this day? Consider it, take counsel, and speak.'"

< Mahukunta 19 >