< Mahukunta 13 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda haka ya ba da su a hannun Filistiyawa shekara arba’in.
Et les enfants d'Israël recommencèrent à faire ce qui déplaît à l'Eternel, et l'Eternel les livra entre les mains des Philistins pendant quarante ans.
2 Akwai wani mutumin Zora, mai suna Manowa, daga kabilar Dan, matarsa kuwa bakararriya ce, ba ta haihuwa.
Or il y avait un homme de Tsorah, d'une famille de ceux de Dan, dont le nom était Manoah, et sa femme était stérile, et n'avait [jamais] eu d'enfant.
3 Mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare ta ya ce, “Ga shi ke bakararriya ce ba kya haihuwa, amma za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa.
Et l'Ange de l'Eternel apparut à cette femme-là, et lui dit: Voici, tu es stérile, et tu n'as [jamais] eu d'enfant; mais tu concevras, et enfanteras un fils.
4 To, sai ki lura kada ki sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye, kada kuma ki ci wani abu marar tsarki,
Prends donc bien garde dès maintenant de ne point boire de vin ni de cervoise, et de ne manger aucune chose souillée.
5 gama za ki yi ciki, ki haifi ɗa. Aska ba za tă taɓa kansa ba, domin yaron zai zama Banazare, keɓaɓɓe ga Allah tun daga haihuwa, shi ne kuwa zai soma ceton Isra’ilawa daga hannuwan Filistiyawa.”
Car voici, tu vas être enceinte, et tu enfanteras un fils, et le rasoir ne passera point sur sa tête; parce que l'enfant sera Nazarien de Dieu dès le ventre [de sa mère]; et ce sera lui qui commencera à délivrer Israël de la main des Philistins.
6 Sa’an nan matar ta tafi wajen mijinta ta faɗa masa cewa, “Wani mutumin Allah ya zo wurina. Ya yi kama da mala’ikan Allah, yana da bantsoro ƙwarai. Ban tambaye shi inda ya fito ba, kuma bai gaya mini sunansa ba.
Et la femme vint, et parla à son mari, en disant: Il est venu auprès de moi un homme de Dieu, dont la face est semblable à la face d'un Ange de Dieu, fort vénérable, mais je ne l'ai point interrogé d'où il était et il ne m'a point déclaré son nom.
7 Sai dai ya ce mini, ‘Za ki yi ciki, ki kuma haifi ɗa. To, fa, kada ki sha ruwan inabi ko abu mai sa maye kada kuma ki ci abin da yake marar tsarki, gama ɗan zai zama Banazare na Allah tun daga haihuwa har ranar mutuwarsa.’”
Mais il m'a dit: Voici, tu vas être enceinte, et tu enfanteras un fils. Maintenant donc ne bois point de vin ni de cervoise, et ne mange aucune chose souillée; car cet enfant sera Nazarien de Dieu dès le ventre [de sa mère] jusqu'au jour de sa mort.
8 Sai Manowa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, bari mutumin Allahn da ka aiko mana yă sāke zuwa don yă koya mana yadda za mu goyi yaron da za a haifa.”
Et Manoah pria instamment l'Eternel, et dit: Hélas, Seigneur! que l'homme de Dieu que tu as envoyé, vienne encore, je te prie, vers nous, et qu'il nous enseigne ce que nous devons faire à l'enfant, quand il sera né.
9 Allah ya ji Manowa, sai mala’ikan Allah ya sāke zuwa wurin matar yayinda take gona; amma Manowa mijinta ba ya tare da ita.
Et Dieu exauça la prière de Manoah. Ainsi l'Ange de Dieu vint encore à la femme comme elle était assise dans un champ; mais Manoah son mari n'était point avec elle.
10 Sai matar ta ruga don ta faɗa wa mijinta, ta ce, “Ga shi ya zo! Mutumin da ya bayyana mini ran nan!”
Et la femme courut vite le rapporter à son mari, en lui disant: Voici, l'homme qui était venu l'autre jour vers moi, m'est apparu.
11 Manowa ya tashi ya bi matarsa. Da ya zo wurin mutumin, sai ya ce, “Kai ne wanda ka yi magana da matata?” Ya ce, “Ni ne.”
Et Manoah se leva, et suivit sa femme; et venant vers l'homme, il lui dit: Es-tu cet homme qui a parlé à cette femme-ci? Et il répondit: C'est moi.
12 Saboda haka Manowa ya tambaye shi ya ce, “Sa’ad da maganarka ta cika, me za tă zama dokar rayuwar yaron da kuma aikinsa?”
Et Manoah dit: Tout ce que tu as dit arrivera; [mais] quel ordre faudra-t-il tenir envers l'enfant, et que lui faudra-t-il faire?
13 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Dole matarka ta kiyaye duk abin da na riga na gaya mata.
Et l'Ange de l'Eternel répondit à Manoah: La femme se gardera de toutes les choses dont je l'ai avertie.
14 Kada tă ci kowane iri abin da ya fito daga inabi, ba kuwa za tă sha ruwan inabi, ko abu mai sa maye ko ta ci abu marar tsarki ba. Dole tă kiyaye duk abin da na umarce mata.”
Elle ne mangera rien qui sorte de la vigne, [rien en quoi il y ait] du vin; et elle ne boira ni vin ni cervoise, et ne mangera aucune chose souillée. Elle prendra garde à tout ce que je lui ai commandé.
15 Manowa ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Muna roƙonka ka jira mu yanka maka ɗan akuya.”
Alors Manoah dit à l'Ange de l'Eternel: Je te prie, que nous te retenions, et nous t'apprêterons un chevreau de lait.
16 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ko kun sa na tsaya, ba zan ci abincinku ba. Amma in kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa wa Ubangiji.” (Manowa bai gane cewa mala’ikan Ubangiji ne ba.)
Et l'Ange de l'Eternel répondit à Manoah: Quand tu me retiendrais je ne mangerais point de ton pain; mais si tu fais un holocauste, tu l'offriras à l'Eternel. Or Manoah ne savait point que ce fût l'Ange de l'Eternel.
17 Sa’an nan Manowa ya sāke tambayi mala’ikan Ubangiji ya ce, “Mene ne sunanka, don mu girmama ka sa’ad da maganarka ta tabbata.”
Et Manoah dit à l'Ange de l'Eternel: Quel est ton nom, afin que nous te fessions un présent lorsque ce que tu as dit sera arrivé?
18 Ya ce, “Me ya sa kake tambaya sunana? Ai, ya wuce fahimta.”
Et l'Ange de l'Eternel lui dit: Pourquoi t'enquiers-tu ainsi de mon nom? car il est admirable.
19 Sa’an nan Manowa ya ɗauki ɗan akuya, tare da hadaya ta hatsi ya miƙa wa Ubangiji a kan dutse. Ubangiji kuwa ya yi abin mamaki yayinda Manowa da matarsa suke kallo.
Alors Manoah prit un chevreau de lait, et un gâteau, et les offrit à l'Eternel sur le rocher. Et l'Ange fit une chose merveilleuse à la vue de Manoah et de sa femme.
20 Yayinda harshen wuta ya yi sama daga bagaden, sai mala’ikan Ubangiji ya haura cikin harshen wutar. Da ganin wannan Manowa da matarsa suka fāɗi da fuskokinsu har ƙasa.
C'est, que la flamme montant de dessus l'autel vers les cieux, l'Ange de l'Eternel monta aussi avec la flamme de l'autel; ce que Manoah et sa femme ayant vu ils se prosternèrent le visage contre terre.
21 Da mala’ikan Ubangiji bai ƙara bayyana kansa ga Manowa da matarsa ba, sai Manowa ya gane cewa mala’ikan Ubangiji ne.
Et l'Ange de l'Eternel n'apparut plus à Manoah ni à sa femme. Alors Manoah connut que c'était l'Ange de l'Eternel.
22 Ya ce wa matar, “Ba shakka za mu mutu, gama mun ga Allah!”
Et Manoah dit à sa femme: Certainement nous mourrons, parce que nous avons vu Dieu.
23 Amma matar ta ce, “Da Ubangiji yana nufin kashe mu ne, da ba zai karɓi hadaya ta ƙonawa da hadaya ta hatsi daga hannunmu, ko yă nuna mana dukan waɗannan abubuwa ko abin da ya gaya mana ba.”
Mais sa femme lui répondit: Si l'Eternel nous eût voulu faire mourir, il n'aurait pas pris de notre main l'holocauste ni le gâteau, et il ne nous aurait pas fait voir toutes ces choses, en un temps comme celui-ci, ni fait entendre les choses que nous avons entendues.
24 Matar kuwa ta haifi ɗa, aka sa masa suna Samson. Ya yi girma Ubangiji kuma ya albarkace shi,
Puis cette femme enfanta un fils, et elle l'appela Samson; et l'enfant devint grand, et l'Eternel le bénit.
25 Ruhun Ubangiji kuwa ya fara iza shi yayinda yake a Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.
Et l'Esprit de l'Eternel commença de le saisir à Mahané-dan, entre Tsorah et Estaol.

< Mahukunta 13 >