< Yoshuwa 9 >

1 To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
Lorsque ces nouvelles parvinrent aux rois des Amorrhéens de la rive droite du fleuve, à ceux de la montagne, à ceux du plat pays, à ceux de la côte de la grande mer, à ceux qui avoisinent l'Anti-Liban et aux Hettéens, aux Chananéens, aux Phérézéens, aux Evéens, aux Amorrhéens, aux Gergéeens et aux Jébuséens,
2 suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
Ils se réunirent à la fois pour combattre Josué et Israël.
3 Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
En ce temps-là, les habitants de Gabaon ouïrent ce que le Seigneur avait fait de Jéricho et d'Haï.
4 sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
Eux aussi usèrent d'artifice; ils se pourvurent de vivres, se tinrent prêts et partirent, ayant lié sur leurs épaules de vieux sacs, de vieilles outres de vin déchirées.
5 Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
Le tour de leurs chaussures ainsi que leurs sandales étaient usés et rapiécés; leurs vêtements montraient la corde, et le pain de leur approvisionnement était desséché, moisi, rongé.
6 Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
Ils vinrent ainsi auprès de Josué, au camp d'Israël en Galgala, et ils dirent à Josué et à Israël: Nous arrivons d'une contrée lointaine, et maintenant faites avec nous une alliance.
7 Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
Aussitôt, les fils d'Israël dirent à l'Horréen: Prenez garde; n'habitez- vous pas notre territoire? En ce cas, comment pourrions-nous faire alliance avec vous?
8 Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
Mais ils répondirent à Josué: Nous sommes tes esclaves. Et Josué leur dit: D'ou êtes-vous? et d'ou venez-vous?
9 Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
Ils reprirent: Tes esclaves arrivent d'une contrée très-lointaine, au nom du Seigneur ton Dieu; car nous avons ouï son nom, nous avons appris tout ce qu'il a fait en Egypte,
10 da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
Et comment il a traité les rois des Amorrhéens qui étaient au delà du fleuve: Séhon, roi des Amorrhéens, et Og, roi de Basan, qui demeurait en Astaroth et en Edraïn.
11 Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
A ces nouvelles, nos anciens et tous ceux qui habitent notre contrée nous ont dit: Prenez avec vous des vivres pour la route, allez à leur rencontre, et dites-leur: Nous sommes vos esclaves, et maintenant faites avec nous une alliance.
12 Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
Voici nos pains qui étaient chauds quand nous nous en sommes approvisionnés, le jour où nous sommes partis pour venir près de vous; ils sont maintenant desséchés et rongés.
13 Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
Et ces outres de vin que nous avons remplies neuves, vous les voyez déchirées; cependant, nos vêtements et nos chaussures se sont usés durant notre bien long voyage.
14 Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
Alors, les chefs d'Israël prirent de ces provisions, et ils n'interrogèrent point le Seigneur.
15 Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
Josué leur accorda donc la paix; il fit avec eux une alliance qui les préserva de tout dommage, et les chefs de la synagogue leur prêtèrent serment.
16 Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
Trois jours après la conclusion de l'alliance, on leur apprit que c'étaient des voisins, et qu'ils habitaient leur territoire.
17 Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
Ensuite, les fils d'Israël levèrent leur camp, et eux allèrent à leurs villes; or, leurs villes étaient Gabaon, Caphira, Beroth et Cariathiarim.
18 Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
Mais les fils d'Israël ne les combattirent point, parce que tous les chefs leur avaient prêté serment, au nom du Seigneur Dieu d'Israël. Et tout le peuple se prit à murmurer contre les chefs.
19 Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
Et les chefs dirent à tout le peuple: Nous leur avons prêté serment au nom du Seigneur Dieu d'Israël, et maintenant nous ne pouvons les toucher.
20 Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
Voici ce que nous ferons: accordons-leur la vie et réservons-les, et il n'y aura point contre nous de colère, à cause du serment que nous leur avons prêté.
21 Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
Ils vivront et ils seront les fendeurs de bois, les porteurs d'eau de toute la synagogue, comme les chefs le leur ont dit.
22 Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
Et Josué, les ayant appelés auprès de lui, leur dit: Pourquoi m'avez-vous trompé, disant: Nous sommes très-éloignés de toi; tandis que vous êtes de ceux qui habitent le territoire qui nous appartient?
23 Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
Maintenant, vous voici nappés de malédiction; jamais vous ne cesserez d'être esclaves, fendeurs de bois, porteurs d'eau à mon service et au service de mon Dieu.
24 Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
Et ils répondirent à Josué, disant: On nous a rapporté que le Seigneur ton Dieu a prescrit à Moïse, son serviteur, de prendre possession de cette terre et d'exterminer devant vous, nous et tous ceux qui l'habitent; à votre approche, nous avons donc été remplis de crainte pour notre vie, et nous avons fait cette chose.
25 Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
Maintenant, voilà que nous sommes en vos mains; faites de nous ce qui vous sera agréable, ce que vous jugerez à propos.
26 Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
Or, voilà ce qu'on fit à leur égard: ce jour-là même, Josué les retira des mains des fils d'Israël, et ceux-ci ne les tuèrent point;
27 A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.
Et ce jour-là même, Josué en fit des fendeurs de bois, des porteurs d'eau pour tout le peuple, et pour l'autel du Seigneur. A cause de cela, les Gabaonites devinrent fendeurs de bois et porteurs d'eau pour l'autel du Seigneur; ils le sont encore de nos jours, et ils doivent servir au lieu qu'aura choisi le Seigneur.

< Yoshuwa 9 >