< Yoshuwa 6 >

1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
Forsothe Jerico was closid and wardid, for the drede of the sones of Israel, and no man durste entre, ethir go out.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
And the Lord seide to Josue, Lo! Y yaf in to thin hondis Jerico, and the king therof, and alle strong men.
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
Alle ye fiyteris, cumpasse the citee onys bi the day; so ye schulen do in sixe daies.
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
Forsothe in the seuenthe dai the preestis schulen take seuene clariouns, of whiche `the vss is in iubile; and thei schulen go bifor the arke of boond of pees; and seuen sithes ye schulen cumpasse the citee, and the preestis schulen trumpe with clariouns.
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
And whanne the vois of the trumpe schal sowne lengere, and more bi whiles, and schal sowne in youre eeris, al the puple schal crie togidere with gretteste cry; and the wallis of the citee schulen falle alle doun, and alle men schulen entre bi the place, ayens which thei stonden.
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
Therfor Josue, the sone of Nun, clepide preestis, and seide to hem, Take ye the ark of boond of pees, and seuene othere preestis take seuene clariouns of iubile yeeris, and go thei bifor the arke of the Lord.
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
Also Josue seide to the puple, Go ye, and cumpasse ye the citee, and go ye armed bifor the arke of the Lord.
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
And whanne Josue hadde endid the wordis, and seuene preestis trumpiden with seuen clariouns bifor the arke of boond of pees of the Lord,
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
and al the puple armed yede bifore, the tothir comyn puple of fiyteris suede the arke, and alle thingis sowneden with clariouns.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
Sotheli Josue comaundide to the puple, and seide, Ye schulen not crye, nethir youre vois schal be herd, nethir ony word schal go out of youre mouth, til the dai come, in which Y schal seie to you, Crye ye, and make ye noyse.
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
Therfor the arke of the Lord cumpasside the citee onys bi day, and turnede ayen in to the castels, and dwellide there.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
Therfor while Josue roos bi nyyt, preestis tooken the arke of the Lord;
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
and seuene of the preestis token seuen clariouns, of whiche `the vss is in iubilee, and yeden bifor the arke of the Lord, `and yeden, and trumpiden; and the puple yede armed bifor hem. Sotheli the tother comyn puple suede the arke, and sownede with clariouns.
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
And thei cumpassiden the citee in the secunde dai onys, and turneden ayen in to the castels; so thei dyden in sixe daies.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
Sotheli in the seuenthe dai thei risiden eerli, and cumpassiden the citee, as it was disposid, seuen sithis.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
And whanne in the seuenthe cumpas preestis sowneden with clariouns, Josue seide to al Israel, Crie ye, for the Lord hath bitake the citee to vs;
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
and this citee be cursid, ethir distried, and alle thingis that ben therynne be halewid to the Lord. Raab the hoor aloone lyue, with alle men that ben with hir in the hows; for sche hidde the messangeris whiche we senten.
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
Forsothe be ye war, lest ye touchen ony thing of these that ben comaundid to you, and ye ben gilti of trespassyng; and alle the castels of Israel be vndur synne, and be troblid.
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
Sotheli what euer thing is of gold, and of siluer, and of brasun vessels, and of yrun, be halewid to the Lord, and be kept in hise tresoris.
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
Therfor while al the puple criede, and the trumpis sowneden, aftir that the sowne sownede in the eeris of the multitude, the walles felden doun anoon; and ech man stiede bi the place that was ayens hym. And thei token the citee,
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
and killiden alle thingis that weren therynne, fro man `til to womman, fro yong child `til to eld man; also thei smytiden bi the scharpnesse of swerd, oxun, and scheep, and assis.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
Forsothe Josue seide to twei men, that weren sent aspieris, Entre ye in to the hows of the womman hoore, and brynge ye forth hir, and alle thingis that ben herne, as ye maden stedfast to hir bi an ooth.
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
And the yonge men entriden, and ledden out Raab, and her fadir, and modir, and britheren, and al the purtenaunce of houshold, and the kynrede `of hir; and maden to dwelle without the castels of Israel.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
Sotheli thei brenten the citee, and alle thingis that weren foundun therynne, without gold, and siluer, and brasun vesselis, and yrun, which thei halewiden in to the `treserie of the Lord.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
Sotheli Josue made Raab the hoore to lyue, and `the hows of hir fadir, and alle thingis that sche hadde; and thei dwelliden in the myddis of Israel, `til in to present dai; for sche hidde the messangeris, whiche he sente to asspie Jerico. In that tyme Josue preiede hertli,
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
and seide, Cursid bifor the Lord be the man, that reisith and bildith the citee of Jerico! Leie he the foundementis therof in his firste gendrid sone, and putte he the yatis therof in the laste of fre children.
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
Therfor the Lord was with Josue, and his name was pupplischid in ech lond.

< Yoshuwa 6 >