< Yoshuwa 21 >

1 To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
Les chefs de familles des Lévites se présentèrent devant le pontife Eléazar, Josué, fils de Noun, et les chefs de familles des tribus d’Israël,
2 Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
à Silo, dans le pays de Canaan, et leur parlèrent ainsi: "L’Eternel a ordonné, par l’organe de Moïse, qu’on nous donnât des villes pour y habiter, ainsi que leurs banlieues pour notre bétail."
3 Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
Et les enfants d’Israël, se conformant à l’ordre du Seigneur, donnèrent aux Lévites, sur leurs parts de possession, les villes suivantes avec leurs ban-lieues.
4 Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
On tira au sort pour les familles des Kehathites; et d’abord, les Lévites, descendants du pontife Aaron, obtinrent, par la voie du sort, dans les tribus de Juda, de Siméon et de Benjamin, treize villes.
5 Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
Le surplus des enfants de Kehath reçut au sort, dans les familles de la tribu d’Ephraïm, dans la tribu de Dan et dans la demi-tribu de Manassé, dix villes.
6 Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
Les enfants de Gerson reçurent au sort, dans les familles de la tribu d’Issachar, dans celles d’Aser et de Nephtali, et dans la demi-tribu de Manassé en Basan, treize villes.
7 Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
Les enfants de Merari, selon leurs familles, eurent de la tribu de Ruben, de celles de Gad et de Zabulon, douze villes.
8 Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Les enfants d’Israël donnèrent ces villes avec leurs banlieues aux Lévites par la voie du sort, comme l’Eternel l’avait prescrit par l’organe de Moïse.
9 Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
De la tribu de Juda et de celle de Siméon, l’on donna les villes suivantes, ainsi désignées nominativement,
10 (ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
pour appartenir aux descendants d’Aaron, d’entre les familles Kehathites, de la tribu de Lévi, à qui échut le premier lot.
11 an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
On leur donna donc la Cité d’Arba (père d’Anok), appelée aussi Hébron, dans la montagne de Juda, avec la banlieue d’alentour.
12 Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
Les champs et les bourgades dépendant de la ville, on les avait donnés comme propriété à Caleb, fils de Yefounné.
13 Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
Mais aux descendants du pontife Aaron l’on donna la ville même de Hébron avec sa banlieue comme ville de refuge pour le meurtrier; plus, Libna avec sa banlieue,
14 da Yattir, da Eshtemowa,
Yattir avec sa banlieue, Echtemoa avec la sienne,
15 da Holon, da Debir,
Holôn avec sa banlieue, Debir avec la sienne,
16 da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
Ayin avec sa banlieue, Youtta avec sa banlieue et Beth-Chémech avec la sienne: neuf villes, remises par les deux tribus en question.
17 Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
Et de la tribu de Benjamin: Gabaon et sa banlieue, Ghéba et la sienne,
18 Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Anatot et sa banlieue, Almôn et la sienne: quatre villes.
19 Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
Total des villes données aux prêtres descendants d’Aaron: treize villes, avec leurs banlieues.
20 Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
Quant aux familles lévitiques descendant de Kehath, formant le surplus des Kehathites, elles eurent au sort les villes suivantes de la tribu d’Ephraïm:
21 A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
on leur donna la ville de refuge destinée au meurtrier, Sichem avec sa banlieue, dans la montagne d’Ephraïm; Ghézer, avec sa banlieue;
22 Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Kibçaïm avec la sienne, Béthorôn avec la sienne: quatre villes.
23 Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
Puis, de la tribu de Dan: Elteké et sa banlieue, Ghibetôn et sa banlieue.
24 Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Ayyalôn et la sienne, Gath-Rimmôn et la sienne: quatre villes.
25 Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
Et de la demi-tribu de Manassé: Taanakh et sa banlieue, Gath-Rimmôn avec la sienne: deux villes.
26 Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
En tout, dix villes avec leurs banlieues, pour le surplus des familles des Kehathites.
27 Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
Les familles lévitiques descendant de Gerson reçurent: de la demi-tribu de Manassé, la ville de refuge Golân, dans le Basan, avec sa banlieue, et Beéchtera avec la sienne: deux villes.
28 daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
De la tribu d’lssachar: Kichyôn avec sa banlieue, Daberath avec la sienne,
29 Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Yarmout avec sa banlieue, En-Gannim avec la sienne: quatre villes.
30 daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
De la tribu d’Aser: Micheal et sa banlieue, Abdôn et la sienne,
31 Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Helkath et sa banlieue, Rehob et la sienne: quatre villes.
32 daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
Et de la tribu de Nephtali: la ville de refuge Kédech, en Galilée, avec sa banlieue; Hamot-Dor avec sa banlieue, Kartân avec la sienne: trois villes.
33 Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
Total des villes des Gersonites, selon leurs familles: treize villes, avec leurs banlieues.
34 Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
Enfin, les familles descendant de Merari, formant le surplus des Lévites, reçurent de la tribu de Zabulon: Yokneam et sa banlieue, Karta et sa banlieue;
35 Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Dimna et sa banlieue, Nahalal avec la sienne: quatre villes.
36 daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
Et de la tribu de Gad: la ville de refuge Ramoth, en Galaad, avec sa banlieue, Mahanaïm, avec la sienne;
37 Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Hesbon, avec sa banlieue; Yazer, avec la sienne: en tout quatre villes.
38 daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
39 Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
40 Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
Telles sont les villes échues aux familles des Merarites, formant le surplus des familles lévitiques; leur lot comportait donc douze villes.
41 Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
Toutes les villes appartenant aux Lévites parmi les possessions des Israélites se montaient ainsi à quarante-huit villes, indépendamment de leurs banlieues.
42 Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
Chacune de ces villes comprenait la banlieue qui lui sert de zone: règle uniforme pour toutes les villes en question.
43 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
Ainsi l’Eternel donna aux Israélites tout le pays qu’il avait promis par serment à leurs ancêtres; ils en prirent possession et s’y établirent.
44 Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
II les fit jouir d’une sécurité entière, comme il l’avait juré à leurs ancêtres; de tous leurs ennemis, pas un n’avait tenu devant eux: tous, Dieu les avait mis en leur pouvoir.
45 Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.
Aucune ne fit défaut de toutes les faveurs que l’Eternel avait promises à la maison d’Israël: toutes s’accomplirent.

< Yoshuwa 21 >