< Yoshuwa 21 >

1 To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
Then the heads of ancestral houses of the Levites came near to Eleazar the priest, and to Joshua the son of Nun, and to the heads of ancestral houses of the tribes of the children of Israel.
2 Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
They spoke to them at Shiloh in the land of Canaan, saying, "The LORD commanded Moses to give us cities to dwell in, with their suburbs for our livestock."
3 Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
The children of Israel gave to the Levites out of their inheritance, according to the commandment of the LORD, these cities with their suburbs.
4 Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
The lot came out for the families of the Kohathites. The descendants of Aaron the priest, who were of the Levites, had thirteen cities by lot out of the tribe of Judah, out of the tribe of the Simeonites, and out of the tribe of Benjamin.
5 Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
The rest of the descendants of Kohath had ten cities by lot out of the families of the tribe of Ephraim, out of the tribe of Dan, and out of the half-tribe of Manasseh.
6 Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
The descendants of Gershon had thirteen cities by lot out of the families of the tribe of Issachar, out of the tribe of Asher, out of the tribe of Naphtali, and out of the half-tribe of Manasseh in Bashan.
7 Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
The descendants of Merari according to their families had twelve cities by lot out of the tribe of Reuben, out of the tribe of Gad, and out of the tribe of Zebulun.
8 Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
The children of Israel gave these cities with their suburbs by lot to the Levites, as the LORD commanded by Moses.
9 Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
They gave out of the tribe of the descendants of Judah, and out of the tribe of the descendants of Simeon, these cities which are mentioned by name:
10 (ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
and they were for the descendants of Aaron, of the families of the Kohathites, who were of the descendants of Levi; for theirs was the first lot.
11 an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
They gave them Kiriath Arba, named after the father of Anak (that is, Hebron), in the hill country of Judah, with its suburbs around it.
12 Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
But they gave the fields of the city and its villages to Caleb the son of Jephunneh for his possession.
13 Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
To the descendants of Aaron the priest they gave Hebron with its suburbs, the city of refuge for the manslayer, Libnah with its suburbs,
14 da Yattir, da Eshtemowa,
Jattir with its suburbs, Eshtemoa with its suburbs,
15 da Holon, da Debir,
Holon with its suburbs, Debir with its suburbs,
16 da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
Ashan with its suburbs, Juttah with its suburbs, and Beth Shemesh with its suburbs; nine cities out of those two tribes.
17 Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
Out of the tribe of Benjamin, Gibeon with its suburbs, Geba with its suburbs,
18 Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Anathoth with its suburbs, and Almon with its suburbs; four cities.
19 Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
All the cities of the descendants of Aaron, the priests, were thirteen cities with their suburbs.
20 Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
The families of the descendants of Kohath, the Levites, even the rest of the descendants of Kohath, had the cities of their lot out of the tribe of Ephraim.
21 A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
They gave them Shechem with its suburbs in the hill country of Ephraim, the city of refuge for the manslayer, and Gezer with its suburbs,
22 Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Kibzaim with its suburbs, and Beth Horon with its suburbs; four cities.
23 Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
Out of the tribe of Dan, Elteke with its suburbs, Gibbethon with its suburbs,
24 Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Aijalon with its suburbs, Gath Rimmon with its suburbs; four cities.
25 Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
Out of the half-tribe of Manasseh, Taanach with its suburbs, and Beth Shean with its suburbs; two cities.
26 Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
All the cities of the families of the rest of the descendants of Kohath were ten with their suburbs.
27 Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
They gave to the descendants of Gershon, of the families of the Levites, out of the half-tribe of Manasseh Golan in Bashan with its suburbs, the city of refuge for the manslayer, and Be Eshterah with its suburbs; two cities.
28 daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
Out of the tribe of Issachar, Kishion with its suburbs, Daberath with its suburbs,
29 Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Jarmuth with its suburbs, En Gannim with its suburbs; four cities.
30 daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
Out of the tribe of Asher, Mishal with its suburbs, Abdon with its suburbs,
31 Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Helkath with its suburbs, and Rehob with its suburbs; four cities.
32 daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
Out of the tribe of Naphtali, Kedesh in Galilee with its suburbs, the city of refuge for the manslayer, Hammothdor with its suburbs, and Kartan with its suburbs; three cities.
33 Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
All the cities of the Gershonites according to their families were thirteen cities with their suburbs.
34 Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
To the families of the descendants of Merari, the rest of the Levites, out of the tribe of Zebulun, Jokneam with its suburbs, Kartah with its suburbs,
35 Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Rimmon with its suburbs, and Nahalal with its suburbs; four cities.
36 daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
And across the Jordan opposite Jericho, from the tribe of Reuben: a city of refuge for the manslayer, Bezer in the wilderness, on the plateau, with its suburbs, Jahaz with its suburbs,
37 Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
Kedemoth with its suburbs, and Mephaath with its suburbs; four cities.
38 daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
Out of the tribe of Gad, Ramoth in Gilead with its suburbs, the city of refuge for the manslayer, and Mahanaim with its suburbs,
39 Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
Heshbon with its suburbs, Jazer with its suburbs; four cities in all.
40 Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
All these were the cities of the descendants of Merari according to their families, even the rest of the families of the Levites. Their lot was twelve cities.
41 Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
All the cities of the Levites in the midst of the possession of the children of Israel were forty-eight cities with their suburbs.
42 Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
Each of these cities included their suburbs around them. It was this way with all these cities.
43 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
So the LORD gave to Israel all the land which he swore to give to their fathers. They possessed it, and lived in it.
44 Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
The LORD gave them rest all around, according to all that he swore to their fathers. Not a man of all their enemies stood before them. The LORD delivered all their enemies into their hand.
45 Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.
Nothing failed of any good thing which the LORD had spoken to the house of Israel. All came to pass.

< Yoshuwa 21 >