< Yoshuwa 17 >

1 Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
This was the assignment of land for the tribe of Manasseh (who was the firstborn of Joseph)—that is, for Makir, who was Manasseh's firstborn and who himself was the father of Gilead. Makir's descendants were assigned the land of Gilead and Bashan, because Makir had been a man of war.
2 Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
Land was assigned to the rest of the tribe of Manasseh, given to their clans—Abiezer, Helek, Asriel, Shechem, Hepher, and Shemida. These were the male descendants of Manasseh son of Joseph, presented by their clans.
3 Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
Now Zelophehad son of Hepher son of Gilead son of Makir son of Manasseh had no sons, but only daughters. The names of his daughters were Mahlah, Noah, Hoglah, Milkah, and Tirzah.
4 Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
They approached Eleazar the priest, Joshua son of Nun, and the leaders, and they said, “Yahweh commanded Moses to give to us an inheritance along with our brothers.” So, following the commandment of Yahweh, he gave those women an inheritance among the brothers of their father.
5 Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
Ten parcels of land were assigned to Manasseh in Gilead and Bashan, which is on the other side of the Jordan,
6 domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
because the daughters of Manasseh received an inheritance along with his sons. The land of Gilead was assigned to the rest of the tribe of Manasseh.
7 Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
The territory of Manasseh reached from Asher to Mikmethath, which is east of Shechem. Then the border went southward to those living near the spring of Tappuah.
8 (Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
(The land of Tappuah belonged to Manasseh, but the town of Tappuah on the border of Manasseh belonged to the tribe of Ephraim.)
9 Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
The border went down to the brook of Kanah. These cities south of the brook among the towns of Manasseh belonged to Ephraim. The border of Manasseh was on the north side of the brook, and it ended at the sea.
10 Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
The land to the south belonged to Ephraim, and the land to the north was Manasseh's; the sea was the border. On the north side Asher can be reached, and to the east, Issachar.
11 A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
Also in Issachar and in Asher, Manasseh possessed Beth Shan and its villages, Ibleam and its villages, the inhabitants of Dor and its villages, the inhabitants of Endor and its villages, the inhabitants of Taanach and its villages, and the inhabitants of Megiddo and its villages (and the third city is Napheth).
12 Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
Yet the tribe of Manasseh could not take possession of those cities, for the Canaanites continued to live in this land.
13 Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
When the people of Israel grew strong, they put the Canaanites to forced labor, but did not completely drive them out.
14 Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
Then the descendants of Joseph said to Joshua, saying, “Why have you given us only one assignment of land and one portion for an inheritance, since we are a people great in number, and all along Yahweh has blessed us?”
15 Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
Joshua said to them, “If you are a people great in number, go up by yourselves to the forest and there clear the ground for yourselves in the land of the Perizzites and of the Rephaim. Do this, since the hill country of Ephraim is too small for you.”
16 Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
The descendants of Joseph said, “The hill country is not enough for us. But all the Canaanites who live in the valley have chariots of iron, both those who are in Beth Shan and its villages, and those who are in the Valley of Jezreel.”
17 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
Then Joshua said to the house of Joseph—to Ephraim and Manasseh, “You are a people great in number, and you have great power. You must not have only one piece of land assigned to you.
18 amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”
The hill country will also be yours. Though it is a forest, you will clear it and take possession of it to its farthest borders. You will drive out the Canaanites, even though they have chariots of iron, and even though they are strong.”

< Yoshuwa 17 >