< Yoshuwa 15 >

1 An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
Now the lot of the children of Juda by their kindreds was this: From the frontier of Edom, to the desert of Sin southward, and to the uttermost part of the south coast.
2 Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
Its beginning was from the top of the most salt sea, and from the bay thereof, that looketh to the south.
3 zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
And it goeth out towards the ascent of the Scorpion, and passeth on to Sina: and ascendeth into Cadesbarne, and reacheth into Esron, going up to Addar, and compassing Carcaa.
4 Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
And from thence passing along into Asemona, and reaching the torrent of Egypt: and the bounds thereof shall be the great sea, this shall be the limit of the south coast.
5 Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
But on the east side the beginning shall be the most salt sea even to the end of the Jordan: and towards the north, from the bay of the sea unto the same river Jordan.
6 wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
And the border goeth up into Beth-Hagla, and passeth by the north into Beth-Araba: going up to the stone of Boen the son of Ruben.
7 Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
And reaching as far as the borders of Debara from the valley of Achor, and so northward looking towards Galgal, which is opposite to the ascent of Adommin, on the south side of the torrent: and the border passeth the waters that are called the fountain of the sun: and the goings out thereof shall be at the fountain Rogel.
8 Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
And it goeth up by the valley of the son of Ennom on the side of the Jebusite towards the south, the same is Jerusalem: and thence ascending to the top of the mountain, which is over against Geennom to the west in the end of the valley of Raphaim, northward.
9 Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
And it passeth on from the top of the mountain to the fountain of the water of Nephtoa: and reacheth to the towns of mount Ephron: and it bendeth towards Baala, which is Cariathiarim, that is to say, the city of the woods.
10 Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
And it compasseth from Baala westward unto mount Seir: and passeth by the side of mount Jarim to the north into Cheslon: and goeth down into Bethsames, and passeth into Thamna.
11 Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
And it reacheth northward to a part of Accaron at the side: and bendeth to Sechrona, and passeth mount Baala: and cometh into Jebneel, and is bounded westward with the great sea.
12 Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
These are the borders round about of the children of Juda in their kindreds.
13 Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
But to Caleb the son of Jephone he gave a portion in the midst of the children of Juda, as the Lord had commanded him: Cariath-Arbe the father of Enac. which is Hebron.
14 Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
And Caleb destroyed out of it the three sons of Ehac, Sesai and Ahiman. and Tholmai of the race of Enac.
15 Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
And going up from thence he came to the inhabitants of Dabir, which before was called Cariath-Sepher, that is to say, the city of letters.
16 Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
And Caleb said: He that shall smite Cariath-Sepher, and take it, I will give him Axa my daughter to wife.
17 Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
And Othoniel the son of Cenez, the younger brother of Caleb, took it: and he gave him Axa his daughter to wife.
18 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
And as they were going together, she was moved by her husband to ask a field of her father, and she sighed as she sat on her ass. And Caleb said to her: What aileth thee?
19 Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
But she answered: Give me a blessing: thou hast given me a southern and dry land, give me also a land that is watered. And Caleb gave her the upper and the nether watery ground.
20 Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
This is the possession of the tribe of the children of Juda by their kindreds.
21 Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
And the cities from the uttermost parts of the children of Juda by the borders of Edom to the south, were Cabseel and Eder and Jagur,
22 Kina, Dimona, Adada,
And Cina and Dimona and Adada,
23 Kedesh, Hazor, Itnan,
And Cades and Asor and Jethnam,
24 Zif, Telem, Beyalot,
Ziph and Telem and Baloth,
25 Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
New Asor and Carioth, Hesron, which is Asor.
26 Amam, Shema, Molada,
Amam, Sama and Molada,
27 Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
And Asergadda and Hassemon and Bethphelet,
28 Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
And Hasersual and Bersabee and Baziothia,
29 Ba’ala, Iyim, Ezem,
And Baala and Jim and Esem,
30 Eltolad, Kesil, Horma,
And Eltholad and Cesil and Harma,
31 Ziklag, Madmanna, Sansanna,
And Siceleg and Medemena and Sensenna,
32 Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
Lebaoth and Selim and Aen and Remmon: all the cities twenty-nine, and their villages.
33 Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
But in the plains: Estaol and Sarea and Asena,
34 Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
And Zanoe and Engannim and Taphua and Enaim,
35 Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
And Jerimoth and Adullam, Socho and Azeca,
36 Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
And Saraim and Adithaim and Gedera and Gederothaim: fourteen cities, and their villages.
37 Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
Sanan and Hadassa and Magdalgad,
38 Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
Delean and Masepha and Jecthel,
39 Lakish, Bozkat, Eglon,
Lachis and Bascath and Eglon,
40 Kabbon, Lahman, Kitlish,
Chebbon and Leheman and Cethlis,
41 Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
And Gideroth and Bethdagon and Naama and Maceda: sixteen cities, and their villages.
42 Libna, Eter, Ashan,
Labana and Ether and Asan,
43 Yefta, Ashna, Nezib,
Jephtha and Esna and Nesib,
44 Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
And Ceila and Achzib and Maresa: nine cities, and their villages.
45 Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
Accaron with the towns and villages thereof.
46 yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
From Accaron even to the sea: all places that lie towards Azotus and the villages thereof.
47 Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
Azotus with its towns and villages. Gaza with its towns and villages, even to the torrent of Egypt, and the great sea that is the border thereof.
48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
And in the mountain Samir and Jether and Socoth,
49 Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
And Danna and Cariath-senna, this is Dabir:
50 Anab, Eshtemo, Anim,
Anab and Istemo and Anim,
51 Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
Gosen and Olon and Gilo: eleven cities and their villages.
52 Arab, Duma, Eshan,
Arab and Ruma and Esaan,
53 Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
And Janum and Beththaphua and Apheca,
54 Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Athmatha and Cariath-Arbe, this is Hebron and Sior: nine cities and their villages.
55 Mawon, Karmel, Zif, Yutta
Maon and Carmel and Ziph and Jota,
56 Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
Jezrael and Jucadam and Zanoe,
57 Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
Accain, Gabaa and Thamna: ten cities and their villages.
58 Halhul, Bet-Zur, Gedor,
Halhul, and Bessur, and Gedor,
59 Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Mareth, and Bethanoth, and Eltecon: six cities and their villages.
60 Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
Cariathbaal, the same is Cariathiarim, the city of woods, and Arebba: two cities and their villages.
61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
In the desert Betharaba, Meddin and Sachacha,
62 Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
And Nebsan, and the city of salt, and Engaddi: six cities and their villages.
63 Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.
But the children of Juda could not destroy the Jebusite that dwelt in Jerusalem: and the Jebusite dwelt with the children of Juda in Jerusalem until this present day.

< Yoshuwa 15 >