< Yoshuwa 13 >

1 Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
Josué était vieux, avancé en âge; Yahweh lui dit: « Tu es devenu vieux, tu es avancé en âge, et il reste encore un très grand pays à conquérir.
2 “Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
Voici le pays qui reste: tous les districts des Philistins et tout le territoire des Gessuriens,
3 Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
depuis le Schichor qui coule à l'orient de l'Egypte, jusqu'à la frontière d'Accaron vers le nord, contrée qui doit être réputée Chananéenne; les cinq princes des Philistins, celui de Gaza, celui d'Azoth, celui d'Ascalon, celui de Geth et celui d'Accaron; les Hévéens
4 Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
au midi; tout le pays des Chananéens, et Maara qui est aux Sidoniens, jusqu'à Aphec, jusqu'à la frontière des Amorrhéens;
5 da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
le pays des Gébalites, et tout le Liban vers le soleil levant, depuis Baal-Gad au pied du mont Hermon jusqu'à l'entrée de Hamath;
6 “Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
tous les habitants de la montagne, depuis le Liban jusqu'aux eaux de Maséréphoth, savoir tous les Sidoniens: je les chasserai de devant les enfants d'Israël. Seulement partage par le sort ces pays en héritage à Israël, comme je l'ai commandé.
7 ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
Et maintenant répartis ce pays en héritage aux neuf tribus et à la demi-tribu de Manassé. »
8 Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
Avec l'autre moitié, les Rubénites et les Gadites ont reçu leur héritage, que Moïse leur a donné de l'autre côté du Jourdain, à l'orient, comme le leur a donné Moïse, serviteur de Yahweh:
9 Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
depuis Aroër sur le bord du torrent de l'Arnon, et depuis la ville qui est au milieu de la vallée, toute la plaine de Médaba jusqu'à Dibon;
10 da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
toutes les villes de Séhon, roi des Amorrhéens, qui régnait à Hésebon, jusqu'à la frontière des enfants d'Ammon;
11 Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
Galaad, le territoire des Gessuriens et des Machatiens, toute la montagne d'Hermon, et tout Basan, jusqu'à Salécha:
12 wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
tout le royaume d'Og en Basan, qui régnait à Astaroth et à Edraï: c'était le dernier reste des Rephaïm. Moïse battit ces rois et les chassa.
13 Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
Mais les enfants d'Israël ne chassèrent point les Gessuriens et les Machatiens, et Gessur et Machat habitent au milieu d'Israël jusqu'à ce jour.
14 Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
La tribu de Lévi fut la seule à laquelle Moïse ne donna pas d'héritage; les sacrifices faits par le feu devant Yahweh, le Dieu d'Israël, sont son héritage, comme il le lui avait dit.
15 Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
Moïse avait donné à la tribu des fils de Ruben une part selon leurs familles.
16 Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
Ils eurent pour territoire, à partir d'Aroër sur le bord du torrent de l'Arnon, et de la ville située au milieu de la vallée, toute la plaine près de Médaba,
17 zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
Hésebon et toutes ses villes dans la plaine, Dibon, Bamoth-Baal, Beth-Baal-Maon,
18 Yahza, Kedemot, Mefa’at,
Jassa, Cédimoth, Méphaath,
19 Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
Cariathaïm, Sabama, Sarath-Asar dans la montagne de la vallée,
20 Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
Beth-Phogor, les pentes du Phasga, Beth-Jésimoth,
21 dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
toutes les autres villes de la plaine et tout le royaume de Séhon, roi des Amorrhéens, qui régnait à Hésebon: Moïse l'avait battu, lui et les princes de Madian, Evi, Récem, Sur, Hur et Rébé, tributaires de Séhon, qui habitaient le pays.
22 Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
Le devin Balaam, fils de Béor, fut aussi du nombre de ceux que les enfants d'Israël firent périr par l'épée.
23 Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
Ainsi le territoire des fils de Ruben atteignait jusqu'au Jourdain et à son territoire. Tel fut l'héritage — les villes et leurs villages — des fils de Ruben, et leurs familles.
24 Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
Moïse donna à la tribu de Gad, aux fils de Gad, une part selon leurs familles.
25 Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
Ils eurent pour territoire: Jaser, toutes les villes de Galaad, la moitié du pays des enfants d'Ammon, jusqu'à Aroër, qui est vis-à-vis de Rabba,
26 da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
depuis Hésebon jusqu'à Raboth-Masphé et Bétonim, et depuis Manaïm jusqu'à la frontière de Dabir;
27 kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
et, dans la vallée, Beth-Haram, Beth-Nemra, Socoth et Saphon, reste du royaume de Séhon, roi d'Hésebon; le Jourdain et son territoire, jusqu'à l'extrémité de la mer de Cénéreth, de l'autre côté du Jourdain, à l'orient.
28 Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
Tel fut l'héritage — les villes et leurs villages — des fils de Gad, selon leurs familles.
29 Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
Moïse donna à la demi-tribu de Manassé, aux fils de Manassé, une part selon leurs familles.
30 Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
Ils eurent pour territoire, à partir de Manaïm, tout Basan, tout le royaume d'Og, roi de Basan, et tous les bourgs de Jaïr en Basan, soixante villes.
31 da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
La moitié de Galaad, Astaroth et Edraï, villes du royaume d'Og en Basan, furent données aux fils de Machir, fils de Manassé, à la moitié des fils de Machir, selon leurs familles.
32 Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
Telles sont les parts que distribua Moïse, lorsqu'il était dans les plaines de Moab, de l'autre côté du Jourdain, en face de Jéricho, à l'orient.
33 Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.
Mais Moïse ne donna pas d'héritage à la tribu de Lévi; Yahweh, le Dieu d'Israël, est son héritage, comme il le lui a dit.

< Yoshuwa 13 >