< Yoshuwa 11 >

1 Sa’ad da Yabin sarkin Hazor ya ji wannan, sai ya aika saƙo zuwa wurin Yobab sarkin Madon, da sarkin Shimron, da Akshaf,
To když uslyšel Jabín, král Azor, poslal k Jobábovi, králi Mádon, a k králi Simron, a k králi Achzaf,
2 ya kuma aika zuwa ga sarakunan arewa waɗanda suke kan tuddai da kuma waɗanda suke cikin Araba a kudancin Kinneret da cikin filayen kwari, da cikin Nafot Dor a yamma;
I k králům, kteříž bydlili k straně půlnoční na horách i na rovinách ku polední Ceneret, i na rovinách a v krajinách Dor na západ,
3 ya kuma aika zuwa ga Kan’aniyawa a gabas da yamma; da kuma zuwa ga Amoriyawa, Hittiyawa da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke kan tuddai; da kuma Hiwiyawa masu zama a gindin dutsen Hermon a yankin Mizfa.
K Kananejskému na východ i na západ, a k Amorejskému, Hetejskému, Ferezejskému a Jebuzejskému na horách, a k Hevejskému pod horou Hermon v zemi Masfa.
4 Suka fito da dukan rundunansu da keken yaƙi masu yawan gaske, babbar runduna, yawansu ya yi kamar yashin bakin teku.
I vytáhli všickni ti a všecka vojska jejich s nimi, lid mnohý jako písek, kterýž jest na břehu mořském nesčíslný, i koňů i vozů velmi mnoho.
5 Duk sarakunan nan suka haɗa mayaƙansu tare, suka kafa sansani a bakin Ruwayen Meron don su yi yaƙi da Isra’ilawa.
A smluvivše se všickni králové ti, přitáhli a položili se spolu při vodách Merom, aby bojovali proti Izraelovi.
6 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, domin war haka gobe zan ba da dukansu a hannun Isra’ilawa, za su kuwa karkashe su. Za ku gurgunta dawakansu, ku kuma ƙone keken yaƙinsu.”
Řekl pak Hospodin k Jozue: Neboj se jich, nebo zítra o této chvíli vydám všecky tyto k zabití Izraelovi; koňům jejich žily podřežeš, a vozy jejich ohněm spálíš.
7 Sai Yoshuwa da dukan mayaƙan suka auka musu a bakin Ruwayen Meron.
Tedy vytáhl Jozue a s ním všecken lid válečný proti nim k vodám Merom rychle, a udeřili na ně.
8 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
I dal je Hospodin v ruku Izraelovi, a porazili je. I honili je až k Sidonu velikému, a až k vodám Maserefot, a k údolí Masfe na východ, a pobili je, tak že nepozůstavili žádného živého.
9 Yoshuwa ya yi musu yadda Ubangiji ya umarta, ya gurgunta dawakansu, ya kuma ƙone keken yaƙinsu.
A učinil jim Jozue, jakož byl rozkázal jemu Hospodin, koňům jejich žily zpodřezoval, a vozy jejich ohněm popálil.
10 A lokacin nan Yoshuwa ya koma da baya ya ci Hazor da yaƙi, ya kuma kashe sarkinta da takobi. (Hazor ce babbar masarautan ƙasashen nan.)
Potom navrátiv se Jozue téhož času, dobyl Azor, a krále jeho zabil mečem. Azor pak bylo prvé nejznamenitější mezi všemi království těmi.
11 Suka karkashe duk mazaunan ƙasar da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba, suka kuma ƙona Hazor.
Pobili také všecko, cožkoli v něm živo bylo, mordujíce je mečem, tak že nezůstalo žádného živého; Azor pak spálil ohněm.
12 Yoshuwa ya ƙwace masarautun nan duka ya kuma kashe sarakunansu da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta.
Takž podobně učinil všechněm městům králů těch, a všecky krále jejich zjímal Jozue, a zbiv je mečem, vyhladil je, jakož přikázal Mojžíš, služebník Hospodinův.
13 Duk da haka Isra’ilawa ba su ƙone biranen da suke kan tuddai ba, sai Hazor kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
A však žádného města z těch, kteráž ještě zůstala v ohradě své, nespálil Izrael, kromě samého Azor, kteréž spálil Jozue.
14 Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
A všecky loupeže měst těch i hovada rozdělili mezi sebou synové Izraelští; toliko všecky lidi zbili mečem, dokudž nevyhladili jich, nenechavše žádného živého.
15 Yadda Ubangiji ya umarci bawansa Musa, haka Musa ya umarci Yoshuwa, shi kuwa ya yi duk abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Jakož byl přikázal Hospodin Mojžíšovi, služebníku svému, tak přikázal Mojžíš Jozue, a Jozue tak činil; nepominul ničeho toho, což byl přikázal Hospodin Mojžíšovi.
16 Saboda haka Yoshuwa ya cinye ƙasar duka da yaƙi, dukan Negeb, duka yankin Goshen, filayen kwari na yamma, Araba da tuddai na Isra’ila da kwarinta.
A tak vzal Jozue všecku tu zemi, hory i všecku stranu polední, i všecku zemi Gosen, i roviny, i pole, totiž hory Izraelské i roviny jejich,
17 Daga Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa wajajen Seyir, zuwa Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon ƙasa da Dutsen Hermon. Ya kama sarakunansu ya karkashe su.
Od hory Halak, kteráž se táhne do Seir, až k Balgad na rovině Libánské, pod horou Hermon; všecky také krále jejich zjímal, a zbil je i zmordoval.
18 Yoshuwa ya daɗe yana yaƙi da dukan waɗannan sarakuna.
Po mnohé dny Jozue vedl válku se všechněmi těmi králi.
19 Sai Hiwiyawa kaɗai waɗanda suke zama a Gibeyon, sauran ba ko birni ɗaya da ta yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka ci dukansu da yaƙi.
A nebylo města, ješto by v pokoj vešlo s syny Izraelskými, kromě Hevejských obyvatelů v Gabaon; jiná všecka válkou vzali.
20 Gama Ubangiji ne ya taurare zukatansu waɗannan sarakuna suka yi yaƙi da Isra’ilawa don yă hallaka su gaba ɗaya, yă gamar da su ba jinƙai, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Nebo od Hospodina to bylo, že jsou zatvrdili byli srdce své, tak aby vyšli válečně proti Izraelovi, a aby je v prokletí vydal, a neučinil jim milosti, ale aby je zahubil, jakož přikázal Hospodin Mojžíšovi.
21 A lokacin nan Yoshuwa ya je ya hallaka Anakawa daga ƙasar tudu. Daga Hebron, Debir da Anab. Daga dukan ƙasar tuddai na Yahuda, da kuma dukan ƙasar tudu ta Isra’ila, Yoshuwa ya hallaka su duka da garuruwansu.
Toho pak času přitáhl Jozue a vyplénil Enaky z těch hor, totiž z Hebronu, z Dabir a z Anab, i ze všeliké hory Judské, a ze všeliké hory Izraelské; spolu s městy jejich vyhladil je Jozue.
22 Ba a bar waɗansu Anakawa a harabar Isra’ila ba; sai dai a Gaza, Gat da Ashdod ne aka samu waɗanda suka ragu da rai.
Nezůstal žádný z Enaků v zemi synů Izraelských; toliko v Gáze, v Gát a v Azotu zůstali.
23 Yoshuwa kuwa ya ƙwace dukan ƙasar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ya ba da ita ta zama ƙasar gādo ga Isra’ilawa, kabila-kabila. Ta haka ƙasar ta huta daga yaƙi.
Tak tedy vzal Jozue všecku tu zemi, jakž byl rozkázal Hospodin Mojžíšovi, a dal ji Jozue v dědictví Izraelovi vedlé dílů jejich, po pokoleních jejich. I odpočinula země od válek.

< Yoshuwa 11 >