< Yoshuwa 10 >

1 Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya ji cewa Yoshuwa ya ci Ai da yaƙi ya kuma hallaka ta sarai, ya yi wa Ai da sarkinta abin da ya yi wa Yeriko da sarkinta, mutanen Gibeyon kuwa sun yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, suna kuma zama kusa da su.
And it came to pass, when Adonizedec, king of Jerusalem, heard that Joshua had captured Ai, and devoted it to destruction, as he had done unto Jericho and her king, so, had he done unto Ai and her king, —and that the inhabitants of Gibeon had made peace with Israel and had come into their midst,
2 Shi da mutanensa suka ji tsoron wannan sosai, gama Gibeyon muhimmiyar birni ce, har ma kamar ɗaya daga cikin biranen sarauta, ya ma fi Ai girma, mazanta duka kuwa mayaƙa ne na ƙwarai.
then feared they greatly, because Gibeon was, a great city, as one of the royal cities, —and because, it, was greater than Ai, and, all the men thereof, were mighty:
3 Saboda haka sai Adoni-Zedek sarkin Urushalima ya roƙi Hoham sarkin Hebron, Firam sarkin Yarmut, Yafiya sarkin Lakish da Debir sarki Eglon ya ce,
therefore sent Adonizedec, king of Jerusalem, unto Hoham, king of Hebron, and unto Piram, king of Jarmuth, and unto Japhia, king of Lachish, and unto Debir, king of Eglon, saying:
4 “Ku zo ku taimake ni in kai wa Gibeyon hari. Domin sun yi yarjejjeniya ta salama da Yoshuwa da Isra’ilawa.”
Come up unto me and help me, that we may smite Gibeon, —for it hath made peace with Joshua, and with the sons of Israel.
5 Sai sarakunan nan biyar na Amoriyawa, sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon suka haɗa sojojinsu. Suka je dukansu suka yi shirin kai wa Gibeyon hari.
So they gathered themselves together and came up, even the five kings of the Amorites—the king of Jerusalem, the king of Hebron, the king of Jarmuth, the king of Lachish, the king of Eglon, —they, and all their hosts, —and encamped near Gibeon, and made war against it.
6 Sai mutanen Gibeyon suka aika zuwa wurin Yoshuwa a sansani a Gilgal, “Kada ka juya wa bayinka baya, ka zo da sauri ka cece mu! Ka taimake mu domin sarakunan Amoriyawa duka daga kan tudu sun haɗa ƙarfinsu tare za su tasar mana.”
So the men of Gibeon sent unto Joshua, unto the camp at Gilgal, saying, Do not withhold thy hand from thy servants, —Come up unto us quickly, and save us, and help us, for all the kings of the Amorites that dwell in the hill-country, are gathered together against us.
7 Saboda haka Yoshuwa ya tashi da rundunarsa duka, tare da dukan jarumawansa.
So Joshua went up from Gilgal, he and all the people of war with him, even all the mighty men of valour.
8 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu; na ba ka su a hannunka. Ba waninsu da zai iya tsayayya da kai.”
And Yahweh said unto Joshua: Do not fear because of them, for, into thy hand, have I delivered them, —not a man of them shall stand before thee.
9 Bayan sun yi tafiya dukan dare daga Gilgal, Yoshuwa ya auko musu ba labari.
So then Joshua came in unto them, suddenly, —all the night, came he up, from Gilgal.
10 Ubangiji ya sa suka ruɗe a gaban Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka yi babbar nasara a kansu a Gibeyon. Isra’ilawa suka fafare su a kan hanyar zuwa Bet-Horon suka karkashe su duka har zuwa Azeka da Makkeda.
And Yahweh confused them before Israel, and smote them with a great slaughter at Gibeon, —and chased them along the way that goeth up Beth-horon, and smote them as far as Azekah and as far as Makkedah.
11 Suna guje wa Isra’ilawa suna gangarawa a kan hanyar Bet-Horon har zuwa Azeka, sai Ubangiji ya turo manyan duwatsu daga sararin sama suka karkashe su, waɗanda manyan duwatsun suka kashe sun fi waɗanda Isra’ilawa suka kashe da takobi.
And it came to pass, when they fled from before Israel, they, being on the slope of Beth-horon, that, Yahweh, cast down upon them great stones out of the heavens, as far as Azekah, and they died, —more, were they who died by the hailstones, than they whom the sons of Israel slew with the sword.
12 A ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa a hannun Isra’ilawa, Yoshuwa ya ce wa Ubangiji a gaban Isra’ilawa, “Ke rana, ki tsaya cik a Gibeyon Kai wata, ka je Kwarin Aiyalon.”
Then, spake Joshua unto Yahweh, on the day when Yahweh delivered up the Amorites before the sons of Israel, —yea he said, in the presence of Israel—Thou Sun! in Gibeon, be still, and thou Moon! in the vale of Aijalon.
13 Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya, har sai da al’ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābanta, kamar yadda aka rubuta a cikin littafin Yashar. Rana ta tsaya a sararin sama, ba tă fāɗi ba har kusan yini guda.
So the sun, was still, and, the moon, stayed, until a nation should be avenged on its foes. Is not, that, written in the Book of the Upright? So then the sun stayed in the middle of the heavens, and hastened not to go in, about a whole day.
14 Ba a taɓa ganin abu haka ba ko dā can, ranar da Ubangiji ya saurari mutum. Ba shakka Ubangiji yana yaƙi domin Isra’ilawa.
And there was no day like that—before it or after it, when Yahweh hearkened unto the voice of a man, —in that, Yahweh, himself fought for Israel.
15 Sai Yoshuwa ya koma sansanin Gilgal tare da dukan Isra’ilawa.
So Joshua returned, and all Israel with him, unto the camp at Gilgal.
16 Sarakunan guda biyar suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda.
So these five kings fled, —and hid themselves in a cave, at Makkedah.
17 Lokacin da aka gaya wa Yoshuwa cewa an sami sarakunan nan biyar a ɓoye a cikin kogo a Makkeda.
And it was told Joshua, saying, —The five kings are found, hid in a cave at Makkedah.
18 Sai ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu ku rufe bakin kogon, sai ku sa waɗannan mutane su yi tsaron kogon.
And Joshua said, Roll ye great stones against the mouth of the cave, —and set over it men, to watch them;
19 Amma kada ku tsaya a can! Ku fafari abokan gābanku, ku kai musu hari ta baya, kada ku bari su kai biranensu, gama Ubangiji Allahnku ya ba da su a hannunku.”
but do not, ye, stay, chase after your enemies, so shall ye attack them in the rear, —do not suffer them to enter into their cities, for Yahweh your God hath delivered them into your hand.
20 Saboda haka Yoshuwa da Isra’ilawa suka hallaka su da yawa ƙwarai, amma’yan kaɗan ɗin da suka rage suka tsere zuwa cikin biranensu masu kāriya.
And it came to pass, when Joshua and the sons of Israel had made an end of smiting them with a very great slaughter, until they were spent, then did, the remainder that were left of them, enter into the fortified cities.
21 Dukan rundunar kuma suka dawo sansanin Makkeda tare da Yoshuwa, ba abin da ya same su. Ba wanda ya sāke tsokanar Isra’ilawa.
And all the people returned unto the camp, unto Joshua at Makkedah, in peace, —none sharpened his tongue at any man of the sons of Israel.
22 Yoshuwa ya ce, “Ku buɗe bakin kogon ku kawo mini sarakunan nan guda biyar.”
Then said Joshua, Open ye the mouth of the cave, —and bring out unto me, these five kings, out of the cave.
23 Sai suka kawo sarakunan biyar daga cikin kogo; sarakunan Urushalima, Hebron, Yarmut, Lakish da Eglon.
And they did so, and brought out unto him, these five kings, out of the cave, —namely, the king of Jerusalem, the king of Hebron, the king of Jarmuth, the king of Lachish, the king of Eglon.
24 Sa’ad da aka kawo sarakunan nan wurin Yoshuwa, ya kira dukan Isra’ilawa ya ce wa shugabannin rundunoni waɗanda suke tare da shi, “Ku zo nan ku taka wuyan sarakunan nan.” Sai suka zo suka taka wuyansu.
And it came to pass, when they brought out these kings unto Joshua, that Joshua called for all the men of Israel, and said unto the captains of the men of war who had been with him, Come near, put your feet upon the necks of these kings. So they came near, and put their feet upon the necks of them.
25 Yoshuwa ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ko kuwa ku razana, amma ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Haka Ubangiji zai yi da duk abokan gāban da za ku yi yaƙi da su.”
Then said Joshua unto them: Do not fear, nor be alarmed, —be firm and bold, for, thus and thus, will Yahweh do unto all your enemies, against whom ye do fight.
26 Sai Yoshuwa ya karkashe waɗannan sarakuna guda biyar, ya kuma rataye kowannensu a bisa itace inda jikunansu suka kasance har yamma.
And Joshua smote them after this, and put them to death, and hanged them upon five trees, —and they remained hung on the trees, until the evening,
27 Da yamma Yoshuwa ya ba da umarni a sauko da su daga itatuwan a jefa su cikin kogon da suka ɓuya. Aka sa manyan duwatsu aka rufe bakin kogon, suna a can har wa yau.
And it came to pass, at the time of the going in of the sun, that Joshua gave command, and they took them down off the trees, and cast them into the cave, where they had hid themselves, —and put great stones upon the mouth of the cave, [which remain], until this very day.
28 A ranan nan Yoshuwa ya ci Makkeda da yaƙi. Ya karkashe mutanen tare da sarkinta. Bai bar wani da rai ba. Ya yi wa sarkin Makkeda yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
And Joshua captured, Makkedah, on that day, and smote it with the edge of the sword, and, the king thereof, devoted he to destruction, them and all the souls that were therein, he left no survivor, —but did unto the king of Makkedah, as he had done unto the king of Jericho.
29 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Makkeda zuwa Libna, suka kai mata hari.
And Joshua passed over, and all Israel with him, from Makkedah unto Libnah, —and fought against Libnah;
30 Ubangiji kuma ya ba da ƙasar da sarkinta a hannun Yoshuwa. Yoshuwa ya karkashe kowa ya hallaka birnin, bai bar wani da rai ba. Ya kuma yi wa sarkin yadda ya yi wa sarkin Yeriko.
and Yahweh delivered, it also, into the hand of Israel, with the king thereof, and he smote it with the edge of the sword, with all the souls that were therein, he left therein no survivor, —but did unto the king thereof, as he had done unto the king of Jericho.
31 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Libna zuwa Lakish; suka yi shiri suka kai mata hari.
And Joshua passed over, and all Israel with him, from Libnah unto Lachish, —and encamped against it, and fought against it;
32 Ubangiji ya ba da Lakish a hannun Isra’ilawa, a rana ta biyu kuwa Yoshuwa ya ci nasara a kansu. Ya karkashe duk mutanen birnin ya kuma hallaka birnin, kamar yadda ya yi a Libna.
and Yahweh delivered Lachish into the hand of Israel, and he captured it on the second day, and smote it with the edge of the sword, with all the souls that were therein, —according to all that he had done unto Libnah.
33 Horam sarkin Gezer kuwa ya zo don yă taimaki Lakish, amma Yoshuwa ya haɗa duk da shi da rundunarsa ya ci su da yaƙi, har bai bar waninsu da rai ba.
Then, came up Horam, king of Gezer, to help Lachish, —and Joshua smote him and his people, until he had not left him a survivor.
34 Yoshuwa kuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Lakish zuwa Eglon; suka yi shiri suka kai mata hari.
And Joshua passed over, and all Israel with him, from Lachish unto Eglon, —and they encamped against it, and fought against it;
35 A ranan nan suka ci ƙasar da yaƙi, suka buge ta, suka karkashe kowa da takobi kamar dai yadda suka yi a Lakish.
and captured it on the same day, and smote it with the edge of the sword, and, all the souls that were therein, on that day, devoted he to destruction, —according to all that he had done to Lachish.
36 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka tashi daga Eglon zuwa Hebron suka kai hari a can.
And Joshua went up, and all Israel with him, from Eglon unto Hebron, —and they fought against it;
37 Suka ci birnin da yaƙi, suka karkashe mazaunanta, da sarkin, har da ƙauyukan, ba wanda ya tsira kamar yadda ya yi wa Eglon. Ya hallakar da ita sarai duk da kowane mutum da yake cikinta.
and captured it, and smote it with the edge of the sword, and the king thereof, and all the cities thereof, with all the souls that were therein—he left not a survivor, according to all that he had done to Eglon, —he devoted it to destruction, and all the souls that were therein.
38 Yoshuwa da Isra’ilawa duka suka juya suka kai wa Debir hari,
Then Joshua turned back, and all Israel with him, unto Debir, —and fought against it;
39 suka hallaka birnin, da sarkinta da ƙauyukanta, suka karkashe dukan mazaunan wurin, ba su bar wani da rai ba. Suka yi wa Debir da sarkinta yadda suka yi wa Libna da sarkinta da kuma Hebron.
and captured it, and the king thereof, and all the cities thereof, and smote them with the edge of the sword, and devoted to destruction every soul that was therein, he left not a survivor, —as he had done unto Hebron, so, did he unto Debir, and unto the king thereof, as also he had done unto Libnah, and unto her king.
40 Yoshuwa ya cinye yankin duka da yaƙi, haɗe da na kan tudu, da Negeb, da kwarin yamma, da filayen cikin duwatsu tare da sarakunansu duka. Bai bar wani da rai ba, ya kashe duk wani mai numfashi, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ilawa ya umarta.
So Joshua smote all the land—the hill country, and the south, and the lowland, and the slopes, and all their kings, he left not a survivor, —but, every breathing thing, devoted he to destruction, as Yahweh, God of Israel, had commanded.
41 Yoshuwa ya ci su da yaƙi daga Kadesh Barneya zuwa Gaza, da kuma daga dukan yankin Goshen zuwa Gibeyon.
Yea Joshua smote them, from Kadesh-barnea, even as far as Gaza, —and all the land of Goshen, even as far as Gibeon.
42 Yoshuwa kuwa ya cinye sarakunan nan duka da ƙasashensu gaba ɗaya gama Ubangiji, Allah na Isra’ila ne ya yi yaƙi domin Isra’ilawa.
Yea, all these kings and their land, did Joshua capture at one time, —because, Yahweh, God of Israel, fought for Israel.
43 Yoshuwa kuwa ya dawo da dukan Isra’ilawa zuwa sansani a Gilgal.
And Joshua returned, and all Israel with him, unto the camp at Gilgal.

< Yoshuwa 10 >