< Yohanna 8 >

1 Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
But Jesus went to the Mountain of Olives.
2 Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
And early in the morning he came again into the Temple and all the people came to him and he was seated teaching them.
3 Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
Now the scribes and Pharisees came, with a woman who had been taken in the act of sinning against the married relation;
4 suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
And putting her forward, they said to him, Master, this woman has been taken in the very act of sinning against the married relation.
5 A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
Now in the law Moses gave directions that such women were to be stoned; what do you say about it?
6 Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
They said this, testing him, so that they might have something against him. But Jesus, with his head bent down, made letters on the floor with his finger.
7 Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
But when they went on with their questions, he got up and said to them, Let him among you who is without sin be the first to send a stone at her.
8 Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
And again, with bent head, he made letters on the floor.
9 Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
And when his words came to their ears, they went out one by one, starting with the oldest even to the last, because they were conscious of what was in their hearts: and Jesus was there by himself with the woman before him.
10 Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
Then Jesus got up, and seeing nobody but the woman, he said to her, Where are the men who said things against you? did no one give a decision against you?
11 Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
And she said, No man, Lord. And Jesus said, And I do not give a decision against you: go, and never do wrong again.]
12 Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
Then again Jesus said to them, I am the light of the world; he who comes with me will not be walking in the dark but will have the light of life.
13 Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”
So the Pharisees said to him, The witness you give is about yourself: your witness is not true.
14 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
Jesus said in answer, Even if I give witness about myself, my witness is true, because I have knowledge of where I came from and where I am going; but you have no knowledge of where I come from or of where I am going.
15 Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
You are judging from what you see; I am judging no man.
16 Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
Even if I am judging, my decision is right, because I am not by myself — with me is the Father who sent me.
17 A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
Even in your law it is said that the witness of two men is true.
18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
I give witness about myself and the Father who sent me gives witness about me.
19 Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
Then they said to him, Where is your Father? Jesus said in answer, You have no knowledge of me or of my Father: if you had knowledge of me you would have knowledge of my Father.
20 Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
Jesus said these words in the place where the offerings were stored, while he was teaching in the Temple: but no man took him because his time was still to come.
21 Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
Then he said to them again, I am going away and you will be looking for me, but death will overtake you in your sins. It is not possible for you to come where I am going.
22 Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
So the Jews said, Will he take his life? Is that why he says, Where I go it is not possible for you to come?
23 Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
And he said to them, You are of the earth; I am from heaven: you are of this world; I am not of this world.
24 Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
For this reason I said to you that death will overtake you in your sins: for if you have not faith that I am he, death will come to you while you are in your sins.
25 Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
Then they said to him, Who are you? Jesus said, What I said to you from the first.
26 Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
I have much to say about you and against you: but he who sent me is true and what he has said to me I say to the world.
27 Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
They did not see that his words were about the Father.
28 Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
So Jesus said, When the Son of man has been lifted up by you, then it will be clear to you who I am, and that I do nothing of myself, but say as the Father gave me teaching.
29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
He who sent me is with me; he has not gone from me, because at all times I do the things which are pleasing to him.
30 Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
When he said this a number came to have faith in him.
31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
Then Jesus said to the Jews who had faith in him, If you keep my word, then you are truly my disciples;
32 Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă’yantar da ku.”
And you will have knowledge of what is true, and that will make you free.
33 Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a’yantar da mu?”
They said to him in answer, We are Abraham's seed and have never been any man's servant: why do you say, You will become free?
34 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
And this was the answer Jesus gave them: Truly I say to you, Everyone who does evil is the servant of sin.
35 Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada. (aiōn g165)
Now the servant does not go on living in the house for ever, but the son does. (aiōn g165)
36 Saboda haka in Ɗan ya’yantar da ku, za ku’yantu da gaske.
If then the son makes you free, you will be truly free.
37 Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
I am conscious that you are Abraham's seed; but you have a desire to put me to death because my word has no place in you.
38 Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”
I say the things which I have seen in my Father's house: and you do the things which come to you from your father's house.
39 Suka ce, “To, ai, Ibrahim ne mahaifinmu.” Yesu ya ce, “Da ku’ya’yan Ibrahim ne, da za ku aikata abubuwan da Ibrahim ya yi.
In answer they said to him, Our father is Abraham. Jesus said to them, If you were Abraham's children you would do what Abraham did.
40 Ga shi kun ƙudura, sai kun kashe ni, ni mutumin da ya faɗa muku gaskiyar da na ji daga Allah. Ibrahim bai yi irin waɗannan abubuwa ba.
But now you have a desire to put me to death, a man who has said to you what is true, as I had it from God: Abraham did not do that.
41 Kuna yin abubuwan da ubanku yake yi ne.” Suka ce, “Mu fa ba shegu ba ne. Uba guda kaɗai da muke da shi, shi ne Allah kansa.”
You are doing the works of your father. They said to him, We are true sons of Abraham; we have one Father, who is God.
42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku, da kun ƙaunace ni, gama daga Allah na fito yanzu kuma ga ni nan. Ban zo saboda kaina ba, amma shi ne ya aiko ni.
Jesus said to them, If God was your Father you would have love for me, because it was from God I came and am here. I did not come of myself, but he sent me.
43 Me ya sa ba kwa gane da maganata? Don ba kwa iya jin abin da nake faɗi.
Why are my words not clear to you? It is because your ears are shut to my teaching.
44 Ku na ubanku ne, Iblis, kuna kuwa so ku aikata abin da ubanku yake so. Shi mai kisankai ne tun farko. Ba ruwansa da gaskiya, gama gaskiya ba ta cikinsa. Yayinda yake ƙarya, yana yin halinsa ne, gama shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma.
You are the children of your father the Evil One and it is your pleasure to do his desires. From the first he was a taker of life; and he did not go in the true way because there is no true thing in him. When he says what is false, it is natural to him, for he is false and the father of what is false.
45 Amma domin ina faɗin gaskiya, ba kwa gaskata!
But because I say what is true, you have no belief in me.
46 Akwai waninku da zai iya haƙaƙƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya na faɗa, me ya sa ba kwa gaskata ni?
Which of you is able truly to say that I am a sinner? If I say what is true, why have you no belief in me?
47 Wanda yake na Allah, yakan ji abin da Allah yake faɗi. Abin da ya sa ba kwa jin sa kuwa shi ne don ku ba na Allah ba ne.”
He who is a child of God gives ear to the words of God: your ears are not open to them because you are not from God.
48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Aha, ai, gaskiyarmu da muka ce kai mutumin Samariya ne, kana kuma da aljani.”
The Jews said to him in answer, Are we not right in saying that you are of Samaria and have an evil spirit?
49 Yesu ya ce, “Ni ba mai aljani ba ne, ni dai ina girmama Ubana, ku kuwa ba kwa girmama ni.
And this was the answer of Jesus: I have not an evil spirit; but I give honour to my Father and you do not give honour to me.
50 Ba na nema wa kaina ɗaukaka, amma akwai wani wanda yake neman mini, shi ne kuma alƙali.
I, however, am not in search of glory for myself: there is One who is searching for it and he is judge.
51 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya kiyaye maganata, ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam.” (aiōn g165)
Truly I say to you, If a man keeps my word he will never see death. (aiōn g165)
52 Da jin haka Yahudawa suka ce, “Tabɗi, yanzu kam mun san kana da aljani! Ibrahim ya mutu haka ma annabawa, ga shi kana cewa duk wanda ya kiyaye maganarka ba zai ɗanɗana mutuwa ba sam. (aiōn g165)
The Jews said to him, Now we are certain that you have an evil spirit. Abraham is dead, and the prophets are dead; and you say, If a man keeps my word he will never see death. (aiōn g165)
53 Ka fi Ibrahim mahaifinmu ne? Ya mutu, haka ma annabawa. Wa kake ɗauka kanka ne?”
Are you greater than our father Abraham, who is dead? and the prophets are dead: who do you say that you are?
54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba kome ba ce. Ubana, wanda kuke cewa shi ne Allahnku, shi ne wanda yake ɗaukaka ni.
Jesus said in answer, If I take glory for myself, my glory is nothing: it is my Father who gives me glory, of whom you say that he is your God.
55 Ko da yake ba ku san shi ba, ni dai na san shi. In kuwa na ce ban san shi ba, na zama maƙaryaci kamar ku ke nan, amma na san shi, kuma ina kiyaye maganarsa.
You have no knowledge of him, but I have knowledge of him; and if I said I have no knowledge of him I would be talking falsely like you: but I have full knowledge of him, and I keep his word.
56 Mahaifinku Ibrahim ya yi farin ciki sosai yă sami ganin ranata; ya kuwa gan ta, ya yi murna.”
Your father Abraham was full of joy at the hope of seeing my day: he saw it and was glad.
57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Kai, shekarunka har yanzu ba su kai hamsin tukuna ba fa, har ka ga Ibrahim!”
Then the Jews said to him, You are not fifty years old; have you seen Abraham?
58 Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne!”
Jesus said to them, Truly I say to you, Before Abraham came into being, I am.
59 Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
So they took up stones to send at him: but Jesus got secretly out of their way and went out of the Temple.

< Yohanna 8 >