< Yowel 2 >

1 Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
در صهیون کرنا بنوازید و در کوه مقدس من صدا بلند کنید! تمامی ساکنان زمین بلرزندزیرا روز خداوند می‌آید و نزدیک است.۱
2 rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
روزتاریکی و ظلمت، روز ابرها و ظلمت غلیظ مثل فجر منبسط بر کوهها! امتی عظیم و قوی که مانندآن از ازل نبوده و بعد از این تا سالها و دهرهای بسیار نخواهد بود.۲
3 A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
پیش روی ایشان آتش می‌سوزاند و در عقب ایشان شعله ملتهب می‌گردد. پیش روی ایشان، زمین مثل باغ عدن ودر عقب ایشان، بیابان بایر است و نیز از ایشان احدی رهایی نمی یابد.۳
4 Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
منظر ایشان مثل منظراسبان است و مانند اسب‌سواران می‌تازند.۴
5 Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
مثل صدای ارابه‌ها بر قله کوهها جست و خیزمی کنند؛ مثل صدای شعله آتش که کاه رامی سوزاند؛ مانند امت عظیمی که برای جنگ صف بسته باشند.۵
6 Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
از حضور ایشان قوم هامی لرزند. تمامی رویها رنگ پریده می‌شود.۶
7 Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
مثل جباران می‌دوند، مثل مردان جنگی بر حصارهابرمی آیند و هر کدام به راه خود می‌آیند وطریقهای خود را تبدیل نمی کنند.۷
8 Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
بر یکدیگرازدحام نمی کنند، زیرا هرکس به راه خودمی خرامد. از میان حربه‌ها هجوم می‌آورند وصف های خود را نمی شکنند.۸
9 Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
بر شهرمی جهند، به روی حصارها می‌دوند، به خانه هابرمی آیند. مثل دزدان از پنجره‌ها داخل می شوند.۹
10 A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
از حضور ایشان زمین متزلزل وآسمانها مرتعش می‌شود؛ آفتاب و ماه سیاه می‌شوند و ستارگان نور خویش را باز می‌دارند.۱۰
11 Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
و خداوند آواز خود را پیش لشکر خویش بلند می‌کند، زیرا اردوی او بسیار عظیم است و آنکه سخن خود را بجا می‌آورد، قدیراست. زیرا روز خداوند عظیم و بی‌نهایت مهیب است و کیست که طاقت آن را داشته باشد.۱۱
12 “Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
و لکن الان خداوند می‌گوید با تمامی دل وبا روزه و گریه و ماتم بسوی من بازگشت نمایید.۱۲
13 Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
و دل خود را چاک کنید نه رخت خویش را وبه یهوه خدای خود بازگشت نمایید زیرا که اورئوف و رحیم است و دیرخشم و کثیراحسان و ازبلا پشیمان می‌شود.۱۳
14 Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
که می‌داند که شایدبرگردد و پشیمان شود و در عقب خود برکتی واگذارد، یعنی هدیه آردی و هدیه ریختنی برای یهوه خدای شما.۱۴
15 A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
در صهیون کرنا بنوازید وروزه را تعیین کرده، محفل مقدس را ندا کنید.۱۵
16 A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
قوم را جمع کنید، جماعت را تقدیس نمایید، پیران و کودکان و شیرخوارگان را فراهم آورید. داماد از حجره خود و عروس از حجله خویش بیرون آیند.۱۶
17 Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
کاهنانی که خدام خداوند هستنددر میان رواق و مذبح گریه کنند و بگویند: «ای خداوند بر قوم خویش شفقت فرما و میراث خویش را به عار مسپار، مبادا امت‌ها بر ایشان حکمرانی نمایند. چرا در میان قومها بگویند که خدای ایشان کجا است؟»۱۷
18 Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
پس خداوند برای زمین خود به غیرت خواهد آمد و بر قوم خویش شفقت خواهد نمود.۱۸
19 Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
و خداوند قوم خود را اجابت نموده، خواهدگفت: «اینک من گندم و شیره و روغن را برای شمامی فرستم تا از آنها سیر شوید و شما را بار دیگردر میان امت‌ها عار نخواهم ساخت.۱۹
20 “Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
و لشکرشمالی را از شما دور کرده، به زمین خشک ویران خواهم راند که مقدمه آن بر دریای شرقی وساقه‌اش بر دریای غربی خواهد بود و بوی بدش بلند خواهد شد و عفونتش برخواهد آمد زیراکارهای عظیم کرده است.»۲۰
21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
‌ای زمین مترس! وجد و شادی بنما زیرایهوه کارهای عظیم کرده است.۲۱
22 Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
‌ای بهایم صحرا مترسید زیرا که مرتع های بیابان سبز شد ودرختان میوه خود را آورد و انجیر و مو قوت خویش را دادند.۲۲
23 Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
‌ای پسران صهیون در یهوه خدای خویش وجد و شادی نمایید، زیرا که باران اولین را به اندازه‌اش به شما داده است وباران اول و آخر را در وقت برای شما بارانیده است.۲۳
24 Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
پس خرمن از گندم پر خواهد شد ومعصره‌ها از شیره و روغن لبریز خواهد گردید.۲۴
25 “Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
و سالهایی را که ملخ و لنبه و سوس و سن یعنی لشکر عظیم من که بر شما فرستاده بودم خوردندبه شما رد خواهم نمود.۲۵
26 Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
و غذای بسیارخورده، سیر خواهید شد و اسم یهوه خدای خودرا که برای شما کارهای عجیب کرده است، تسبیح خواهید خواند و قوم من تا به ابد خجل نخواهند شد.۲۶
27 Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
و خواهید دانست که من در میان اسرائیل می‌باشم و من یهوه خدای شما هستم ودیگری نیست و قوم من خجل نخواهند شد تاابدالاباد.۲۷
28 “Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
و بعد از آن روح خود را بر همه بشر خواهم ریخت و پسران و دختران شما نبوت خواهندنمود و پیران شما و جوانان شما رویاها خواهنددید.۲۸
29 Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
و در آن ایام روح خود را بر غلامان وکنیزان نیز خواهم ریخت.۲۹
30 Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
و آیات را از خون وآتش و ستونهای دود در آسمان و زمین ظاهرخواهم ساخت.۳۰
31 Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
آفتاب به تاریکی و ماه به خون مبدل خواهند شد، پیش از ظهور یوم عظیم ومهیب خداوند.۳۱
32 Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.
و واقع خواهد شد هر‌که نام خداوند را بخواند نجات یابد زیرا در کوه صهیون و در اورشلیم چنانکه خداوند گفته است بقیتی خواهد بود و در میان باقی ماندگان آنانی که خداوند ایشان را خوانده است.۳۲

< Yowel 2 >