< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Därefter tog Job till orda och sade:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Ja, förvisso vet jag att så är; huru skulle en människa kunna hava rätt mot Gud?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Vill han gå till rätta med henne, så kan hon ej svara honom på en sak bland tusen.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Han som är så vis i förstånd och så väldig i kraft, vem kan trotsa honom och dock slippa undan;
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
honom som oförtänkt flyttar bort berg och omstörtar dem i sin vrede;
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
honom som kommer jorden att vackla från sin plats, och dess pelare bäva därvid;
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
honom som befaller solen, så går hon icke upp, och som sätter stjärnorna under försegling;
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
honom som helt allena spänner ut himmelen och skrider fram över havets toppar;
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
honom som har gjort Karlavagnen och Orion, Sjustjärnorna och söderns Stjärngemak;
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
honom som gör stora och outrannsakliga ting och under, flera än någon kan räkna?
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Se, han far förbi mig, innan jag hinner att se det, han drager framom mig, förrän jag bliver honom varse.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Se, han griper sitt rov; vem kan hindra honom? Vem kan säga till honom: "Vad gör du?"
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Gud, han ryggar icke sin vrede; för honom har Rahabs följe måst böja sig;
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
huru skulle jag då våga svara honom, välja ut ord till att tala med honom?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Nej, om jag än hade rätt, tordes jag dock ej svara; jag finge anropa min motpart om misskund.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Och om han än svarade mig på mitt rop, så kunde jag ej tro att han lyssnade till min röst.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Ty med storm hemsöker han mig och slår mig med sår på sår, utan sak.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Han unnar mig icke att hämta andan; nej, med bedrövelser mättar han mig.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Gäller det försteg i kraft: "Välan, jag är redo!", gäller det rätt: "Vem ställer mig till ansvar?"
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Ja, hade jag än rätt, så dömde min mun mig skyldig; vore jag än ostrafflig, så läte han mig synas vrång.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Men ostrafflig är jag! Jag aktar ej mitt liv, jag frågar icke efter, om jag får leva.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Det må gå som det vill, nu vare det sagt: han förgör den ostrafflige jämte den ogudaktige.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Om en landsplåga kommer med plötslig död, så bespottar han de oskyldigas förtvivlan.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
Jorden är given i de ogudaktigas hand, och täckelse sätter han för dess domares ögon. Är det ej han som gör det, vem är det då?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Min dagar hasta undan snabbare än någon löpare, de fly bort utan att hava sett någon lycka;
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
de ila åstad såsom en farkost av rör, såsom en örn, när han störtar sig ned på sitt byte.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Om jag än besluter att förgäta mitt bekymmer, att låta min sorgsenhet fara och göra mig glad,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Så måste jag dock bäva för alla mina kval; jag vet ju att du icke skall döma mig fri.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Nej, såsom skyldig måste jag stå där; varför skulle jag då göra mig fåfäng möda?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Om jag än tvår mig i snö och renar mina händer i lutsalt,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
så skall du dock sänka mig ned i pölen, så att mina kläder måste vämjas vid mig.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Ty han är ej min like, så att jag vågar svara honom, ej en sådan, att vi kunna gå till doms med varandra;
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
ingen skiljeman finnes mellan oss, ingen som har myndighet över oss båda.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Må han blott vända av från mig sitt ris, och må fruktan för honom ej förskräcka mig;
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
då skall jag tala utan att rädas för honom, ty jag vet med min själv att jag icke är en sådan.

< Ayuba 9 >