< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Job respondió:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
“¡Sí, todo eso lo sé! Pero, ¿cómo puede alguien tener la razón delante Dios?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Si quisieras discutir con Dios, éste podría hacer mil preguntas que nadie puede responder.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Dios es tan sabio y poderoso que nadie podría desafiarlo y ganarle.
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
“Dios mueve las montañas de repente; las derriba en su ira.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Él sacude la tierra, haciendo temblar sus cimientos.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Él es quien puede ordenar que el sol no salga y que las estrellas no brillen.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Sólo él es quien extiende los cielos y camina sobre las olas del mar.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Él hizo las constelaciones de la Osa, de Orión, de las Pléyades y las estrellas del cielo austral.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Él es quien hace cosas increíbles que están más allá de nuestro entendimiento, cosas maravillosas que son incontables.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
“Pero cuando pasa junto a mí, no lo veo; cuando camina hacia adelante, es invisible para mí.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Si él quita, ¿Quién podrá impedírselo? ¿Quién va a preguntarle: ‘Qué haces’?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Dios no refrena su ira, y aplasta a los ayudantes de Rahab.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
“Así que, ¡cuánto menos podría responder a Dios, o elegir mis palabras para discutir con él!
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Aunque tenga razón, no puedo responderle. Debo implorar la misericordia de mi juez.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Aunque lo llamara para que viniera y él respondiera, no creo que me escuchara.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
“Me golpea con vientos de tormenta; me hiere una y otra vez, sin dar razón.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
No me da la oportunidad ni siquiera de recuperar el aliento; en cambio, llena mi vida de amargo sufrimiento.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Si de fuerza se trata, Dios es el más fuerte. Si es cuestión de justicia, entonces ¿quién fijará un tiempo para mi caso?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Aunque tenga razón, mi propia boca me condenaría; aunque sea inocente, él demostraría que estoy equivocado.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
¡Soy inocente! No me importa lo que me pase. ¡Odio mi vida!
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Por eso digo: ‘A Dios le da igual. Él destruye tanto al inocente como al malvado’.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Cuando el desastre golpea de repente, se burla de la desesperación de los inocentes.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
La tierra ha sido entregada al malvado; él ciega los ojos de los jueces; y si no es él, entonces ¿quién?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Los días de mi vida corren como un corredor, pasando a toda prisa sin que yo vea ninguna felicidad.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Pasan como veloces veleros, como el águila que se abalanza sobre su presa.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
“Si me dijera a mí mismo: ‘Olvidaré mis quejas; dejaré de llorar y seré feliz’,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
seguiría aterrado por todo mi sufrimiento, porque tú, Dios, no dirás que soy inocente.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Ya que estoy condenado, ¿qué sentido tiene discutir?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
¡Aunque me lavara con agua pura de la montaña y me limpiara las manos con jabón,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
me arrojarías a un pozo de lodo de modo que hasta mis propias ropas me odiarían!
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Porque Dios no es un ser mortal como yo, no puedo defenderme ni llevarlo a juicio.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Si hubiera un árbitro ¡que pudiera reunirnos a los dos!
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
¡Ojalá Dios dejara de golpearme con su vara y de aterrorizarme!
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Entonces podría hablar sin tener miedo; pero como lo tengo, no puedo!”

< Ayuba 9 >