< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
Yahweh continued to speak to Job; he said,
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
“Should anyone who wishes to criticize try to correct the Almighty? He who argues with God, let him answer.”
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Then Job answered Yahweh and said,
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
“See, I am insignificant; how can I answer you? I put my hand over my mouth.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
I spoke once, and I will not answer; indeed, twice, but I will proceed no further.”
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
Then Yahweh answered Job out of a fierce storm and said,
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
“Now gird up your loins like a man, for I will ask you questions, and you must answer me.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Will you actually say that I am unjust? Will you condemn me so you may claim you are right?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Do you have an arm like God's? Can you thunder with a voice like him?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Now clothe yourself in glory and dignity; array yourself in honor and majesty.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Scatter around the excess of your anger; look at everyone who is proud and bring him down.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Look at everyone who is proud and bring him low; trample down wicked people where they stand.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Bury them in the earth together; imprison their faces in the hidden place.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Then will I also acknowledge about you that your own right hand can save you.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Look now at the behemoth, which I made when I made you; he eats grass like an ox.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
See now, his strength is in his loins; his power is in his belly's muscles.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
He makes his tail like a cedar; the sinews of his thighs are joined together.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
His bones are like tubes of bronze; his legs are like bars of iron.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
He is the chief of the creatures of God. Only God, who made him, can defeat him.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
For the hills provide him with food; the beasts of the field play nearby.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
He lies under the lotus plants in the shelter of the reeds, in the marshes.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
The lotus plants cover him with their shade; the willows of the brook are all around him.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
See, if a river floods its banks, he does not tremble; he is confident, though the Jordan should surge up to his mouth.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Can anyone capture him with a hook, or pierce his nose through with a snare?

< Ayuba 40 >