< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Je unajua ni wakati gani mbuzi mwitu huzaa watoto wao katika miamba? Je waweza kuwangalia paa wakati wanapozaa watoto wao?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Waweza kuhesabu miezi ya kuchukua mimba? Je unaujua muda ambao huzaa watoto wao?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
Wanainama chini na kuzaa watoto wao, na kisha maumivu yao ya uzazi yanaishi.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Watoto wao huwa na nguvu na kukua katika uwanda wa wazi; hutoka nje na hawarudi tena.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Ni nani huwaacha punda mwitu waende huru? Je nani amevilegeza vifungo vya punda wepesi,
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
ni nyumba ya nani nimeifanya katika Araba, au nyumba yake katika nchi ya chumvi?
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
Hucheka kwa dharau katika kelele katika mji; hasikilizi kelele za mwongozaji.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
Hutembeatembea juu ya milima kama malisho yake; huko hutafuta kila mmea ulio wa kijani kwa ajili ya kula.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Je nyati atakuwa na furaha kukutumikia? Je atakubali kukaa katika zizi lako?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Waweza kumwongoza nyati kulima mtaro kwa kamba? Je atachimba bonde kwa ajili yako?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Je waweza kumtumaini kwasababu ya nguvu zake nyingi? Je waweza kumwachia kazi yako ili aifanye?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Je waweza kumtegemea akuletee nyumbani nafaka, au kukusanya nafaka katika uwanda wako wa kupuria?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
Mabawa ya mbuni hupunga kwa majivuno, bali je mabawa na manyoya yana upendo?
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
Kwa maana huuacha mayai yake katika nchi, na huyaacha yapate joto katika mavumbi;
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
husahau kuwa mguu waweza kuyaharibu au kwamba mnyama mwitu aweza kuyakanyaga.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
Huyatendea vibaya makinda yake kana kwamba si yake; haogopi kwamba kazi yake yaweza kupotea bure,
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
kwasababu Mungu amemnyima hekima na hajampa ufahamu wowote.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
Na wakati anapokimbia kwa haraka, huwacheka kwa dharau farasi na mpanda farasi wake.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Je umempa farasi nguvu zake? Je umeivika shingo yake kwa manyoya?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Je umemfanya aruke kama panzi? Enzi ya mlio wake ni wa kutisha.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
Hurarua kwa nguvu na kufurahia katika nguvu zake; hukimbia upesi kukutana na silaha.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
Huidharau hofu na hashangazwi; huwa harudi nyuma kutoka katika upanga.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Podo hugongagonga ubavuni mwake, pamoja na mkuki unaong'aa na fumo.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
Huimeza nchi kwa hasira na ghadhabu; katika sauti ya tarumbeta, hawezi kusimama sehemu moja.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
Wakati wowote tarumbeta inapolia, husema, 'Ooh! Huisikia harufu ya vita kutoka mbali - vishindo vya radi za makamanda na makelele.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Je ni kwa hekima yako kwamba mwewe hupaa juu, na ya kuwa huyanyosha mabawa yake kwa upande wa kusini?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Je ni kwa agizo lako kwamba tai huruka juu na kufanya kiota chake katika sehemu za juu?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
Huishi katika majabali na hufanya makao yake katika vilele vya majabali, na ngomeni.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
Kutoka huko hutafuta mawindo; macho yake huyaona mawindo kutoka mbali.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Makinda yake hunywa damu pia; na pale walipo watu wafu, ndipo na yeye alipo.

< Ayuba 39 >