< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Sais-tu le temps auquel les chamois des rochers font leurs petits? As-tu observé quand les biches faonnent?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Compteras-tu les mois qu'elles achèvent leur portée, et sauras-tu le temps auquel elles feront leurs petits,
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
Et qu'elles se courberont pour mettre bas leurs petits, [et] qu'elles se délivreront de leurs douleurs?
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Leurs fans se portent bien, ils croissent dans les blés; ils s'écartent, et ne retournent plus vers elles.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Qui est-ce qui a laissé aller libre l'âne sauvage, et qui a délié les liens de l'âne farouche,
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Auquel j'ai donné la campagne pour maison, la terre inhabitée pour ses retraites?
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
Il se rit du bruit de la ville; il n'entend point les clameurs de l'exacteur;
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
Les montagnes qu'il va épiant çà et là, sont ses pâturages, et il cherche toute sorte de verdure.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
La licorne voudra-t-elle te servir, ou demeurera-t-elle à ta crèche?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Lieras-tu la licorne avec son licou pour labourer? ou rompra-t-elle les mottes des vallées après toi?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
T'assureras-tu d'elle, sous ombre que sa force est grande, et lui abandonneras-tu ton travail?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Te fieras-tu qu'elle te porte ta moisson, et qu'elle l'amasse dans ton aire?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
As-tu donné aux paons ce plumage qui est si brillant, ou à l'autruche les ailes et les plumes?
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
Néanmoins elle abandonne ses œufs à terre, et les fait échauffer sur la poussière,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
Et elle oublie que le pied les écrasera, ou que les bêtes des champs les fouleront.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
Elle se montre cruelle envers ses petits, comme s'ils n'étaient pas à elle; et son travail est souvent inutile et elle ne s'en soucie point.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
Car Dieu l'a privée de sagesse, et ne lui a point donné d'intelligence;
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
A la première occasion elle se dresse en haut, et se moque du cheval et de celui qui le monte.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
As-tu donné la force au cheval? [et] as-tu revêtu son cou d'un [hennissement] éclatant comme le tonnerre?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Feras-tu bondir le cheval comme la sauterelle? le son magnifique de ses narines est effrayant.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
Il creuse la terre [de son pied], il s'égaie en sa force, il va à la rencontre d'un homme armé;
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
Il se rit de la frayeur, il ne s'épouvante de rien, et il ne se détourne point de devant l'épée.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
[Il n'a point peur des] flèches qui sifflent tout autour de lui, ni du fer luisant de la hallebarde et du javelot.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
Il creuse la terre, plein d'émotion et d'ardeur au son de la trompette, et il ne peut se retenir.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
Au son bruyant de la trompette, il dit: Ha! ha! Il flaire de loin la bataille, le tonnerre des Capitaines, et le cri de triomphe.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Est-ce par ta sagesse que l'épervier se remplume, et qu'il étend ses ailes vers le Midi?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Sera-ce à ton commandement que l'aigle prendra l'essor, et qu'elle élèvera sa nichée en haut?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
Elle habite sur les rochers, et elle s'y tient; [même] sur les sommets des rochers et dans des lieux forts.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
De là elle découvre le gibier, ses yeux voient de loin.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Ses petits aussi sucent le sang, et où il y a des corps morts, elle y est aussitôt.

< Ayuba 39 >