< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Sais-tu le temps où mettent bas les bouquetins des rochers? As-tu observé les douleurs des biches?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
As-tu compté les mois qu’elles accomplissent, et connais-tu le temps où elles mettent bas?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
Elles se courbent, elles enfantent leur portée, elles se délivrent de leurs douleurs.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Leurs petits deviennent forts, ils grandissent dans les champs, ils s’en vont et ne reviennent pas à elles.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Qui a lâché l’âne sauvage? qui a délié les liens de l’onagre,
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Auquel j’ai donné le désert pour maison, et la terre salée pour demeure?
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
Il se rit du tumulte de la ville, il n’entend pas le cri du conducteur.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
Il parcourt les montagnes pour trouver sa pâture, et il est en quête de tout ce qui est vert.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Le buffle voudra-t-il être à ton service? Passera-t-il la nuit auprès de ta crèche?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Attacheras-tu le buffle par sa corde dans le sillon? Hersera-t-il les vallées après toi?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Auras-tu confiance en lui, parce que sa force est grande, et lui abandonneras-tu ton labeur?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Te fieras-tu à lui pour rentrer ce que tu as semé, et rassemblera-t-il [le blé] dans ton aire?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
L’aile de l’autruche bat joyeusement: ce sont les plumes et le plumage de la cigogne;
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
Toutefois elle abandonne ses œufs à la terre et les chauffe sur la poussière,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
Et elle oublie que le pied peut les écraser et la bête des champs les fouler;
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
Elle est dure avec ses petits comme s’ils n’étaient pas à elle; son labeur est vain, sans qu’elle s’en émeuve.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
Car Dieu l’a privée de sagesse, et ne lui a pas départi l’intelligence.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
Quand elle s’enlève, elle se moque du cheval et de celui qui le monte.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Est-ce toi qui as donné au cheval sa force? Est-ce toi qui as revêtu son cou d’une crinière flottante?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Est-ce toi qui le fais bondir comme la sauterelle? Son ronflement magnifique est terrible.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
Il creuse [le sol] dans la plaine et se réjouit de sa force; il sort à la rencontre des armes;
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
Il se rit de la frayeur et ne s’épouvante pas, et il ne se tourne pas devant l’épée.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Sur lui retentit le carquois, brillent la lance et le javelot.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
Frémissant et agité, il dévore le sol, et ne peut se contenir quand sonne la trompette.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
Au bruit de la trompette, il dit: Ha! ha! et de loin il flaire la bataille, le tonnerre des chefs et le tumulte.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Est-ce par ton intelligence que l’épervier prend son essor et qu’il étend ses ailes vers le midi?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Est-ce à ta parole que l’aigle s’élève et qu’il bâtit haut son aire?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
Il demeure dans les rochers et y fait son habitation, sur la dent du rocher et sur les hautes cimes.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
De là il épie sa nourriture, ses yeux regardent dans le lointain.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Ses petits sucent le sang, et là où sont les tués, là il est.

< Ayuba 39 >