< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Connais-tu le temps où les chèvres sauvages font leurs petits? As-tu observé les biches quand elles mettent bas?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
As-tu compté les mois de leur portée, et connais-tu l’époque de leur délivrance?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
Elles se mettent à genoux, déposent leurs petits, et sont quittes de leurs douleurs.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Leurs faons se fortifient et grandissent dans les champs; ils s’en vont, et ne reviennent plus.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Qui a lâché l’onagre en liberté, qui a brisé les liens de l’âne sauvage,
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
à qui j’ai donné le désert pour maison, pour demeure la plaine salée?
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
Il méprise le tumulte des villes, il n’entend pas les cris d’un maître.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
Il parcourt les montagnes pour trouver sa pâture, il y poursuit les moindres traces de verdure.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Le buffle voudra-t-il te servir, ou bien passera-t-il la nuit dans son étable?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
L’attacheras-tu avec une corde au sillon, ou bien hersera-t-il derrière toi dans les vallées?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Te fieras-tu à lui parce qu’il est très fort, lui laisseras-tu faire tes travaux?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Compteras-tu sur lui pour rentrer ta moisson, pour recueillir le blé dans ton aire?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
L’aile de l’autruche bat joyeusement; elle n’a ni l’aile pieuse ni le plumage de la cigogne.
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
Elle abandonne ses œufs à la terre, et les laisse chauffer sur le sable.
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
Elle oublie que le pied peut les fouler, la bête des champs les écraser.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
Elle est dure pour ses petits, comme s’ils n’étaient pas siens; que son travail soit vain, elle ne s’en inquiète pas.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
Car Dieu lui a refusé la sagesse, et ne lui a pas départi l’intelligence.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
Mais quand elle se bat les flancs et prend son essor, elle se rit du cheval et du cavalier.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Est-ce toi qui donnes au cheval la vigueur, qui revêts son cou d’une crinière flottante,
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
qui le fais bondir comme la sauterelle? Son fier hennissement répand la terreur.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
Il creuse du pied la terre, il est fier de sa force, il s’élance au-devant du combat.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
Il se rit de la peur; rien ne l’effraie; il ne recule pas devant l’épée.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Sur lui résonne le carquois, la lance étincelante et le javelot.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
Il frémit, il s’agite, il dévore le sol; il ne se contient plus quand la trompette sonne.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
Au bruit de la trompette, il dit: « Allons! » De loin il flaire la bataille, la voix tonnante des chefs et les cris des guerriers.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Est-ce par ta sagesse que l’épervier prend son vol et déploie ses ailes vers le midi?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Est-ce à ton ordre que l’aigle s’élève, et fait son nid sur les hauteurs?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
Il habite les rochers, il fixe sa demeure dans les dents de la pierre, sur les sommets.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
De là, il guette sa proie, son regard perce au loin.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Ses petits s’abreuvent de sang; partout où il y a des cadavres, on le trouve.

< Ayuba 39 >