< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Hast thou known the time of The bearing of the wild goats of the rock? The bringing forth of hinds thou dost mark!
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Thou dost number the months they fulfil? And thou hast known the time of their bringing forth!
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
They bow down, Their young ones they bring forth safely, Their pangs they cast forth.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Safe are their young ones, They grow up in the field, they have gone out, And have not returned to them.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Who hath sent forth the wild ass free? Yea, the bands of the wild ass who opened?
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Whose house I have made the wilderness, And his dwellings the barren land,
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He doth laugh at the multitude of a city, The cries of an exactor he heareth not.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
The range of mountains [is] his pasture, And after every green thing he seeketh.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Is a Reem willing to serve thee? Doth he lodge by thy crib?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Dost thou bind a Reem in a furrow [with] his thick band? Doth he harrow valleys after thee?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Dost thou trust in him because great [is] his power? And dost thou leave unto him thy labour?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Dost thou trust in him That he doth bring back thy seed? And [to] thy threshing-floor doth gather [it]?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
The wing of the rattling ones exulteth, Whether the pinion of the ostrich or hawk.
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
For she leaveth on the earth her eggs, And on the dust she doth warm them,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
And she forgetteth that a foot may press it, And a beast of the field tread it down.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
Her young ones it hath hardened without her, In vain [is] her labour without fear.
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
For God hath caused her to forget wisdom, And He hath not given a portion To her in understanding:
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
At the time on high she lifteth herself up, She laugheth at the horse and at his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Dost thou give to the horse might? Dost thou clothe his neck [with] a mane?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Dost thou cause him to rush as a locust? The majesty of his snorting [is] terrible.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
They dig in a valley, and he rejoiceth in power, He goeth forth to meet the armour.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He laugheth at fear, and is not affrighted, And he turneth not back from the face of the sword.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
Against him rattle doth quiver, The flame of a spear, and a halbert.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
With trembling and rage he swalloweth the ground, And remaineth not stedfast Because of the sound of a trumpet.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
Among the trumpets he saith, Aha, And from afar he doth smell battle, Roaring of princes and shouting.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
By thine understanding flieth a hawk? Spreadeth he his wings to the south?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
At thy command goeth an eagle up high? Or lifteth he up his nest?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
A rock he doth inhabit, Yea, he lodgeth on the tooth of a rock, and fortress.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
From thence he hath sought food, To a far off place his eyes look attentively,
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
And his brood gulp up blood, And where the pierced [are] — there [is] he!

< Ayuba 39 >