< Ayuba 39 >

1 “Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
Knowest thou the time when the wild goats of the rock bring forth? [or] canst thou mark when the hinds do calve?
2 Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
Canst thou number the months [that] they fulfill? or knowest thou the time when they bring forth?
3 Suna kwanciya su haifi’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
They bow themselves, they bring forth their young ones, they cast out their sorrows.
4 ’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
Their young ones are in good liking, they grow up with corn; they go forth, and return not to them.
5 “Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
Who hath sent out the wild ass free? or who hath loosed the bands of the wild ass?
6 Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Whose house I have made the wilderness, and the barren land his dwellings.
7 Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
He scorneth the multitude of the city, neither regardeth he the crying of the driver.
8 Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
The range of the mountains [is] his pasture, and he searcheth after every green thing.
9 “Ko ɓauna zai yarda yă zauna a wurin sa wa dabbobi abinci? Zai tsaya a ɗakin dabbobinka da dare?
Will the unicorn be willing to serve thee, or abide by thy crib?
10 Ko za ka iya daure shi da igiya a kwarin kunya? Zai yi maka buɗar gonarka?
Canst thou bind the unicorn with his band in the furrow? or will he harrow the valleys after thee?
11 Ko za ka dogara da shi don yawan ƙarfinsa? Za ka bar masa nauyin aikinka?
Wilt thou trust him, because his strength [is] great? or wilt thou leave thy labor to him?
12 Ko za ka amince da shi yă kawo maka hatsinka gida yă tattara shi a masussuka?
Wilt thou believe him, that he will bring home thy seed, and gather [it into] thy barn?
13 “Fikafikan jimina suna bugawa cike da farin ciki amma ba za su gwada kansu da fikafikan da na shamuwa ba.
[Gavest thou] the goodly wings to the peacocks? or wings and feathers to the ostrich!
14 Tana sa ƙwai nata a ƙasa kuma ta bar su su yi ɗumi a cikin ƙasa,
Which leaveth her eggs in the earth, and warmeth them in the dust,
15 ba tă damu ko za a taka su a fasa su, ko waɗansu manyan dabbobi za su tattake su.
And forgetteth that the foot may crush them, or that the wild beast may break them.
16 Tana tsananta wa’ya’yanta kamar ba nata ba ba tă damu da wahalar da ta sha ba.
She is hardened against her young ones, as though [they were] not hers: her labor is in vain without fear;
17 Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
Because God hath withheld wisdom from her, neither hath he imparted to her understanding.
18 Duk da haka sa’ad da ta buɗe fikafikanta ta shara da gudu tana yi wa doki da mai hawansa dariya.
When she lifteth herself on high, she scorneth the horse and his rider.
19 “Ko kai ne kake ba doki ƙarfinsa kai kake rufe wuyansa da geza mai yawa?
Hast thou given the horse strength? hast thou clothed his neck with thunder?
20 Ko kai kake sa shi yă yi tsalle kamar fāra, ba ya jin tsoro sai dai a ji tsoronsa.
Canst thou make him afraid as a grasshopper? the glory of his nostrils [is] terrible.
21 Yana takawa da ƙarfi yana jin daɗin ƙarfinsa yana shiga filin yaƙi gabagadi.
He paweth in the valley, and rejoiceth in [his] strength: he goeth on to meet the armed men.
22 Yana yi wa tsoro dariya ba ya jin tsoron kome; ba ya guje wa takobi.
He mocketh at fear, and is not affrighted; neither turneth he back from the sword.
23 Kwari a baka yana lilo a gabansa kibiya da māshi suna wuce kansa.
The quiver rattleth against him, the glittering spear and the shield.
24 Yana kartar ƙasa da ƙarfi; ba ya iya tsayawa tsab sa’ad da ya ji busar ƙaho.
He swalloweth the ground with fierceness and rage: neither believeth he that [it is] the sound of the trumpet.
25 Da jin ƙarar ƙaho sai ya ce, ‘Yauwa!’ Ya ji ƙanshin yaƙi daga nesa, da ihun shugabannin yaƙi.
He saith among the trumpets, Ha, ha; and he smelleth the battle afar off, the thunder of the captains, and the shouting.
26 “Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
Doth the hawk fly by thy wisdom, [and] stretch her wings towards the south?
27 Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
Doth the eagle mount up at thy command, and make her nest on high?
28 Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
She dwelleth and abideth on the rock, upon the crag of the rock, and the strong place.
29 Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
From thence she seeketh the prey, [and] her eyes behold afar off.
30 ’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Her young ones also suck up blood: and where the slain [are], there [is] she.

< Ayuba 39 >