< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
Elihu continued on and said,
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
“Permit me to speak a little longer, and I will show you some things because I have a little more to say in defense of God.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
I will obtain my knowledge from far off; I will acknowledge that righteousness belongs to my Maker.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
For indeed, my words will not be false; someone who is mature in knowledge is with you.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
See, God is mighty, and despises no one; he is mighty in strength of understanding.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
He does not preserve the life of wicked people but instead does what is right for those who suffer.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
He does not withdraw his eyes from righteous people but instead sets them on thrones like kings forever, and they are lifted up.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
If they are bound in chains and trapped in cords of suffering,
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
then he reveals to them what they have done, and their transgressions and their pride.
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
He also opens their ears to his instruction, and commands them to turn back from iniquity.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
If they listen to him and worship him, they will spend their days in prosperity, their years in contentment.
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
However, if they do not listen, they will perish by the sword; they will die because they have no knowledge.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Those who are godless in heart store up their anger; they do not cry out for help even when God ties them up.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
They die in their youth; their lives end among the cultic prostitutes.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
God rescues afflicted people by means of their afflictions; he opens their ears by means of their oppression.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
Indeed, he would like to draw you out of distress into a broad place where there is no hardship and where your table would be set with food full of fatness.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
But you are full of judgment on wicked people; judgment and justice have laid hold of you.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
Do not let your anger entice you to mockery, or the greatness of a ransom to turn you aside.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
Can your wealth benefit you, so that you will not be in distress, or can all the force of your strength help you?
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
Do not desire the night, to commit sin against others, when peoples are cut off in their place.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Be careful that you do not turn to sin because you are being tested by suffering so that you will stay away from sinning.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
See, God is exalted in his power; who is a teacher like him?
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
Who has ever instructed him about his way? Who can ever say to him, 'You have committed unrighteousness?'
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
Remember to praise his deeds, of which people have sung.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
All people have looked on those deeds, but they see those deeds only from far away.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
See, God is great, but we do not understand him well; the number of his years is incalculable.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
For he draws up the drops of water that he distills as rain from his vapor,
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
which the clouds pour down and drop in abundance on mankind.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
Indeed, can anyone understand the extensive spread of the clouds and the thunder from his hut?
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
See, he spreads his lightning around him and covers the roots of the sea.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
In this way he judges the peoples and gives food in abundance.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
He fills his hands with the lightning until he commands it to strike its mark.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
Its thunder warns of the storm, the cattle can also hear it is coming.

< Ayuba 36 >