< Ayuba 34 >

1 Sa’an nan Elihu ya ce,
Et Élihu reprit la parole et dit:
2 “Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Sages, écoutez mes paroles, et vous qui avez de la connaissance, prêtez-moi l’oreille;
3 Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
Car l’oreille éprouve les discours, comme le palais goûte les aliments.
4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Choisissons pour nous ce qui est juste, et reconnaissons entre nous ce qui est bon.
5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
Car Job a dit: Je suis juste, et Dieu a écarté mon droit;
6 Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
Mentirai-je contre ma droiture? ma blessure est incurable, sans qu’il y ait de transgression.
7 Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
Qui est l’homme qui soit comme Job? Il boit la moquerie comme l’eau;
8 Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
Il marche dans la compagnie des ouvriers d’iniquité, et il chemine avec les hommes méchants.
9 Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
Car il a dit: Il ne profite de rien à l’homme de trouver son plaisir en Dieu.
10 “Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
C’est pourquoi, hommes de sens, écoutez-moi: Loin de Dieu la méchanceté, et loin du Tout-puissant l’iniquité!
11 Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
Car il rendra à l’homme ce qu’il aura fait, et il fera trouver à chacun selon sa voie.
12 Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
Certainement Dieu n’agit pas injustement, et le Tout-puissant ne pervertit pas le droit.
13 Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
Qui a confié la terre à ses soins, et qui a placé le monde entier [sous lui]?
14 In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
S’il ne pensait qu’à lui-même et retirait à lui son esprit et son souffle,
15 ’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
Toute chair expirerait ensemble et l’homme retournerait à la poussière.
16 “In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
Si [tu as] de l’intelligence, écoute ceci; prête l’oreille à la voix de mes paroles.
17 Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
Celui qui hait la justice gouvernera-t-il donc? Et condamneras-tu le juste par excellence?
18 Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
Dira-t-on Bélial, au roi? – Méchants, aux nobles?
19 wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
[Combien moins] à celui qui ne fait pas acception de la personne des princes, et qui n’a pas égard au riche plutôt qu’au pauvre; car ils sont tous l’œuvre de ses mains.
20 Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
Ils mourront en un moment; au milieu de la nuit les peuples chancellent et s’en vont, et les puissants sont retirés sans main.
21 “Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
Car ses yeux sont sur les voies de l’homme, et il voit tous ses pas.
22 Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
Il n’y a pas de ténèbres, il n’y a pas d’ombre de la mort, où puissent se cacher les ouvriers d’iniquité.
23 Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
Car il ne pense pas longtemps à un homme pour le faire venir devant Dieu en jugement.
24 Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
Il brise les puissants, sans examen, et il fait que d’autres se tiennent à leur place;
25 Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
En effet il connaît leurs œuvres: il les renverse de nuit, et ils sont écrasés.
26 Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
Il les frappe comme des méchants dans le lieu où ils sont en vue,
27 domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
Parce qu’ils se sont retirés de lui, et qu’ils n’ont pas considéré toutes ses voies,
28 Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
Pour faire monter vers lui le cri du pauvre, en sorte qu’il entende le cri des malheureux.
29 Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
Quand il donne la tranquillité, qui troublera? Il cache sa face, et qui le verra? [Il fait] ainsi, soit à une nation, soit à un homme,
30 yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
Pour empêcher l’homme impie de régner, pour écarter du peuple les pièges.
31 “A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
Car a-t-il [jamais] dit à Dieu: Je porte ma peine, je ne ferai plus de mal;
32 Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
Ce que je ne vois pas, montre-le-moi; si j’ai commis l’iniquité, je ne le referai pas?
33 Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
Rétribuera-t-il selon tes pensées? car tu as rejeté [son jugement], car toi, tu as choisi, et non pas moi; ce que tu sais, dis-le donc.
34 “Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
Les hommes de sens me diront, et un homme sage qui m’écoute:
35 ‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
Job n’a pas parlé avec connaissance, et ses paroles ne sont pas intelligentes;
36 Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
Je voudrais que Job soit éprouvé jusqu’au bout, parce qu’il a répondu à la manière des hommes iniques;
37 Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”
Car il a ajouté à son péché la transgression; il bat des mains parmi nous, et multiplie ses paroles contre Dieu.

< Ayuba 34 >