< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
Et maintenant, je suis la risée d'hommes plus jeunes que moi, dont je n'aurais pas daigné mettre les pères parmi les chiens de mon troupeau.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Qu'aurais-je fait de la force de leurs bras? Ils sont privés de toute vigueur.
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
Desséchés par la misère et la faim, ils broutent le désert, un sol depuis longtemps aride et désolé.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
Ils cueillent sur les buissons des bourgeons amers, ils n'ont pour pain que la racine des genêts.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
On les écarte de la société des hommes, on crie après eux comme après le voleur.
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
Ils habitent dans d'affreuses vallées, dans les cavernes de la terre et les rochers.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
On entend leurs cris sauvages parmi les broussailles, ils se couchent ensemble sous les ronces:
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
gens insensés, race sans nom, bannis avec mépris de la terre habitée!
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
Et maintenant je suis l'objet de leurs chansons, je suis en butte à leurs propos.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Ils ont horreur de moi, ils me fuient, ils ne détournent pas leur crachat de mon visage.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
Ils se donnent libre carrière pour m'outrager, ils rejettent tout frein devant moi.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
Des misérables se lèvent à ma droite, ils cherchent à ébranler mes pieds, ils frayent jusqu'à moi leurs routes meurtrières.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
Ils ont bouleversé mes sentiers, ils travaillent à ma ruine, eux à qui personne ne porterait secours.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
Ils fondent sur moi, comme par une large brèche, ils se précipitent parmi les décombres.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Les terreurs m'assiègent, ma prospérité est emportée comme un souffle, mon bonheur a passé comme un nuage.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
Et maintenant, mon âme s'épanche en moi, les jours d'affliction m'ont saisi.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
La nuit perce mes os, les consume, le mal qui me ronge ne dort pas.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
Par sa violence, mon vêtement a perdu sa forme, il me serre comme une tunique.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
Dieu m'a jeté dans la fange, je suis comme la poussière et la cendre.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Je crie vers toi, et tu ne me réponds pas; je me tiens debout, et tu me regardes avec indifférence.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Tu deviens cruel à mon égard, tu m'attaques avec toute la force de ton bras.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Tu m'enlèves, tu me fais voler au gré du vent, et tu m'anéantis dans le fracas de la tempête.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Car, je le sais, tu me mènes à la mort, au rendez-vous de tous les vivants.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Cependant celui qui va périr n'étendra-t-il pas les mains et, dans sa détresse, ne poussera-t-il pas un cri?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
N'avais-je pas des larmes pour l'infortuné? Mon cœur ne s'est-il pas attendri sur l'indigent?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
J'attendais le bonheur, et le malheur est arrivé; j'espérais la lumière, et les ténèbres sont venues.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
Mes entrailles bouillonnent sans relâche, les jours d'affliction ont fondu sur moi.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
Je marche dans le deuil, sans soleil; si je me lève dans l'assemblée, c'est pour pousser des cris.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
Je suis devenu le frère des chacals, le compagnon des filles de l'autruche.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Ma peau livide tombe en lambeaux, mes os sont brûlés par un feu intérieur.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Ma cithare ne rend plus que des accords lugubres, mon chalumeau que des sons plaintifs.

< Ayuba 30 >