< Ayuba 30 >

1 “Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
“But now those who are younger than I have me in derision, whose fathers I considered unworthy to put with my sheep dogs.
2 Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
Of what use is the strength of their hands to me, men in whom ripe age has perished?
3 Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
They are gaunt from lack and famine. They gnaw the dry ground, in the gloom of waste and desolation.
4 A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
They pluck salt herbs by the bushes. The roots of the broom tree are their food.
5 An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
They are driven out from among men. They cry after them as after a thief,
6 An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
so that they live in frightful valleys, and in holes of the earth and of the rocks.
7 Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
They bray among the bushes. They are gathered together under the nettles.
8 Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
They are children of fools, yes, children of wicked men. They were flogged out of the land.
9 “Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
“Now I have become their song. Yes, I am a byword to them.
10 Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
They abhor me, they stand aloof from me, and don’t hesitate to spit in my face.
11 Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
For he has untied his cord, and afflicted me; and they have thrown off restraint before me.
12 A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
On my right hand rise the rabble. They thrust aside my feet. They cast their ways of destruction up against me.
13 Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
They mar my path. They promote my destruction without anyone’s help.
14 Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
As through a wide breach they come. They roll themselves in amid the ruin.
15 Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Terrors have turned on me. They chase my honor as the wind. My welfare has passed away as a cloud.
16 “Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
“Now my soul is poured out within me. Days of affliction have taken hold of me.
17 Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
In the night season my bones are pierced in me, and the pains that gnaw me take no rest.
18 A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
My garment is disfigured by great force. It binds me about as the collar of my tunic.
19 Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
He has cast me into the mire. I have become like dust and ashes.
20 “Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
I cry to you, and you do not answer me. I stand up, and you gaze at me.
21 Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
You have turned to be cruel to me. With the might of your hand you persecute me.
22 Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
You lift me up to the wind, and drive me with it. You dissolve me in the storm.
23 Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
For I know that you will bring me to death, to the house appointed for all living.
24 “Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
“However doesn’t one stretch out a hand in his fall? Or in his calamity therefore cry for help?
25 Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
Didn’t I weep for him who was in trouble? Wasn’t my soul grieved for the needy?
26 Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
When I looked for good, then evil came. When I waited for light, darkness came.
27 Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
My heart is troubled, and doesn’t rest. Days of affliction have come on me.
28 Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
I go mourning without the sun. I stand up in the assembly, and cry for help.
29 Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
I am a brother to jackals, and a companion to ostriches.
30 Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
My skin grows black and peels from me. My bones are burned with heat.
31 Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.
Therefore my harp has turned to mourning, and my pipe into the voice of those who weep.

< Ayuba 30 >