< Ayuba 3 >

1 Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
After this Job opened his mouth, and cursed his day.
2 Ayuba ya ce,
Job answered:
3 “A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
"Let the day perish in which I was born, the night which said, 'A man is conceived.'
4 Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
Let that day be darkness. May God above not care about it, neither let the light shine on it.
5 Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
Let darkness and the shadow of death claim it for their own. Let a cloud dwell on it. Let the blackness of the day terrify it.
6 Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
As for that night, let thick darkness seize on it. Let it not rejoice among the days of the year. Let it not come into the number of the months.
7 Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
Look, let that night be barren. Let no joyful voice come in it.
8 Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
Let them curse it who curse the day, who are ready to rouse up leviathan.
9 Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
Let the stars of its twilight be dark. Let it look for light, but have none, neither let it see the eyelids of the morning,
10 gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
because it did not shut up the doors of my mother's womb, nor did it hide trouble from my eyes.
11 “Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
"Why did I not die from the womb? Why did I not give up the spirit when my mother bore me?
12 Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
Why did the knees receive me? Or why the breast, that I should suck?
13 Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
For now should I have lain down and been quiet. I should have slept, then I would have been at rest,
14 tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
with kings and counselors of the earth, who built up waste places for themselves;
15 da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
or with princes who had gold, who filled their houses with silver:
16 Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
or as a hidden untimely birth I had not been, as infants who never saw light.
17 A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
There the wicked cease from troubling. There the weary are at rest.
18 Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
There the prisoners are at ease together. They do not hear the voice of the taskmaster.
19 Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
The small and the great are there. The servant is free from his master.
20 “Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
"Why is light given to him who is in misery, life to the bitter in soul,
21 ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
Who long for death, but it doesn't come; and dig for it more than for hidden treasures,
22 waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
who rejoice exceedingly, and are glad, when they can find the grave?
23 Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
Why is light given to a man whose way is hid, whom God has hedged in?
24 Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
For my sighing comes before I eat. My groanings are poured out like water.
25 Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
For the thing which I fear comes on me, That which I am afraid of comes to me.
26 Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
I am not at ease, neither am I quiet, neither have I rest; but trouble comes."

< Ayuba 3 >